Dakarun Gwagwarmayar Yemen Sun Kai Hare-Haren Daukan Fansa Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Published: 19th, April 2025 GMT
Dakarun gwagwarmayar Yemen sun kaddamar da hare-haren daukan fansa kan yankin Jaffa da ke kusa da birnin Tel Aviv na Isra’ila
Dakarun gwagwarmayar Yemen sun sanar da aiwatar da wasu matakan soji masu inganci kan yankin Jaffa da aka mamaye, da kuma kan jiragen ruwan Amurka masu dauke da jiragen saman yaki na Truman da Vinson, gami da harbo jirgin sama kiran MQ-9.
Dakarun gwagwarmayar sun bayyana a cikin wata sanarwa da Birgediya Janar Yahya Sar’ie ya bayyana a tsakanin miliyoyin mutane a dandalin Al-Sabeen a ranar Juma’a cewa: Sun kai wani harin soji a kusa da filin jirgin saman Ben Gurion a yankin Jaffa da aka mamaye da makami mai linzami na “Zulfiqar”. Dakarun kasar ta Yemen sun tabbatar da cewa suna ci gaba da gudanar da mummunan arangama a tsawon kusan watanni biyu da kuma kalubalantar hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar Yemen a matakin mayar da martani da kalubalantar hare-haren wuce gona da iri kan kasarsu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinwan Akalla 16 Sojojin HKI Suka Kashe A Gaza Ya Zuwa Yanzu A Yau Laraba
Majiyar kungiyoyin bada taimakon gaggawa a Gaza sun bayyana cewa ya zuwa lokacin bada wannan labarin a yau Laraba, sojojin yahudawan Sahyoniyya sun kashe akalla mutane 16.
Shafin labarai na Arab News ta kasar Saudia ya nakalto Mahmud Bassal kakakin wata kungiyar bada agaji na Gaza yana cewa da misalign karfe biyun dare jiragen yakin HKI sun kai hare-hare kan gidan Osama Al-arbeed dan jarida mai daukar hotuna a gidansa da ke arewacin Gaza, inda harin ya raunata Osman Arbeed sannan ya kashe wasu daga cikin yan gidansa.
Har’ila yau wasu mutane 6 sun kai ga shahada a yayinda wasu 15 suka ji rauni daga ciki har da yara kanana, a garin Khan Yunus a safiyar yau Laraba. A lokacin da kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa ya tuntubi sojojin HKI dangane da wadannan hare-haren basu bada amsa ba.
A cikin watan da ya gabata ne gwamnatin Natanyahu ta kara yawan hare-hare a gaza, na nufin samun abinda ya kira cikekken Nasara a kan Hamas a gaza. Don haka ne sojojin HJI suke kashe falasdinawa gwargwadon iyawarsu a Gaza a ko wace rana.