Cibiyar Nazarin Jinsi (CGS) Da Jami’ar Bayero Kano Za Su Yi Aiki Tare
Published: 17th, April 2025 GMT
Cibiyar Nazarin Jinsi (CGS) Jami’ar Bayero Kano BUK ta jaddada aniyar ta na ci gaba da ayyukan da suka shafi jinsi ta hanyar sabunta aikinta da kuma inganta karfinta na ma’aikata.
Darakta CGS, Dakta Ambasada Safiya Nuhu, ta bayyana haka a lokacin da ta kai ziyarar ban girma ga Shugaban jami’ar Farfesa Sagir Adamu Abbas.
Ta ba da tabbacin mataimakiyar shugabar gudanarwa ta CG ta ci gaba da ba da goyon baya wajen tinkarar al’amuran al’umma, musamman wajen karfafa dabi’un iyali, inganta al’adun gargajiya, da kuma haifar da kyakkyawar tarbiyya.
Dokta Safiya ta jaddada cewa sabbin nade-naden mukaman da aka yi wa mataimakan daraktoci na cibiyar na nuni da yadda jami’ar ta yi hadin gwiwa wajen tunkarar kalubalen da ke addabar al’umma ta hanyar binciken da ya shafi jinsi da hada kan al’umma.
Ta bayyana cewa Cibiyar za ta yi bikin cika shekaru 10 a shekarar 2025 kuma ta kara himma a shirye-shiryen horarwa, bincike, hadin gwiwa, da ayyuka masu tasiri.
“Wani sanannen haɗin gwiwa shine shirin “Ilimi don Canji”, ƙoƙari na haɗin gwiwa tare da jami’o’i a Kanada da Uganda da nufin magance matsalolin da suka danganci jinsi ta hanyar bincike da haɓaka iyawa”
A nasa jawabin, Shugaban jami’ar Farfesa Sagir Adamu Abbas ya yabawa cibiyar kan sababbin ayyukanta.
Farfesa Sagir ya kwadaitar da cibiyar da ta binciko sabbin hanyoyin magance kalubalen da mata da matasa ke fuskanta a wannan zamani da suka hada da shaye-shayen miyagun kwayoyi, da kuma yin amfani da kwarewarta wajen samun kudade na ciki da waje domin dorewa.
Rel/Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da aniyar ta ta bunƙasa harkar kiwon dabbobi a Nijeriya a matsayin wata muhimmiyar hanya ta magance rikice-rikicen da ke tsakanin manoma da makiyaya, tare da amfani da damar tattalin arzikin da ke cikin ɓangaren.
Ɗaya daga cikin Shugabannin Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Gyaran Harkar Kiwo, Farfesa Attahiru Jega, shi ne ya bayyana hakan a wurin taron tattaunawa tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasa, wanda Gidauniyar Sa Ahmadu Bello ta shirya a Kaduna, a ranar Laraba.
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyarJega ya bayyana cewa sabuwar Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo tana ɗaya daga cikin ginshiƙan da ke cikin shirin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na sauya fasalin ɓangaren kiwon dabbobi.
Ya jaddada cewa ana aiwatar da hangen nesa na Shugaban Ƙasa ba tare da son rai na siyasa ba, tare da mayar da hankali kan haɗa kai da duk masu ruwa da tsaki, ciki har da gwamnatocin jihohi, sarakunan gargajiya, al’ummomin makiyaya da sauran muhimman masu ruwa da tsaki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp