Mali, Nijar, da Burkina Faso sun janye jakadunsu daga Algeria
Published: 8th, April 2025 GMT
Kasashen Mali, Nijar, da Burkina Faso sun janye jakadunsu daga kasa Algeria bayan takaddamar da ta barke tsakaninta da Mali.
Kasashen uku da ke karkashin mulkin soja sun sanar da daukar wannan matakin hadin gwiwa ne bayan Mali ta zargi sojojin Algeria da harbo wani jirginta mara matuki a sararin samaniyarta a karshen watan Maris.
A ranar 1 ga Afrilu, Algeria ta sanar cewa ta harbo wani jirgin sama mara matuki mai dauke da makamai a sararin samaniyarta, amma ba ta yi karin bayanin ba.
A cikin wata sanarwa, Ma’aikatar Harkokin Wajen Mali ta ce hukumomi sun tabbatar da “cikakken yakini” cewa an harbo jirgin ne a cikin “A matsayin harin makiya da aka shirya daga gwamnatin Algeria.”
Gobara ta kona motoci 10 a garejin Borno Express Kisan Janar Alƙali: Kotu ta ɗage shari’a zuwa 28 ga MayuSanarwar ta ce an gano burbushin jirgin kilomita 9.5 kudu da iyakar Algeria kuma an harbo shi ne da “makami mai linzami.”
Da take bayyana shi a matsayin “abin da bai taba faruwa ba na cin zarafi,” sanarwar ta ce Mali “ta yi Allah wadai da kakkausan harshe game da wannan aikin makiya, rashin abokantaka, da kuma nuna girman kai daga hukumomin Algeria.”
Algeria ba ta yi wani tsokaci nan take game da janye jakadun ba, amma ta sanar a ranar Litinin cewa ta rufe sararin samaniyarta ga jiragen sama da ke zuwa ko tafiya Mali.
Ma’aikatar tsaron Algeria ta ce, “Saboda yawan keta hurumin sararin samaniyarmu da Mali ke yi, gwamnatin Algeria ta yanke shawarar rufe zirga-zirgar jiragen sama da ke zuwa ko tafiya Mali, tun daga yau.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jirgi mara matuki Nijar Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
Sun ce suna tafiya daga Yola zuwa Lafia ne lokacin da wasu mutane da ake zargin ‘yan fashi ko masu garkuwa da mutane ne suka kai musu hari, lamarin da ya sa suka tsere zuwa daji don tsira rayukansu.
Sojojin sun taimaka wajen gyara tayar motar sannan suka tabbatar da cewa fasinjojin sun ci gaba da tafiyarsu cikin tsaro.
Shugaban Runduna ta 6, Birgediya Janar Kingsley Uwa, ya yaba wa sojojin bisa saurin ɗaukar mataki da kuma tsayin daka kan aiki.
Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai a kan lokaci domin taimakawa wajen yaƙi da laifuka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp