Aminiya:
2025-06-15@08:17:38 GMT

Mali, Nijar, da Burkina Faso sun janye jakadunsu daga Algeria

Published: 8th, April 2025 GMT

Kasashen Mali, Nijar, da Burkina Faso sun janye jakadunsu daga kasa Algeria bayan takaddamar da ta barke tsakaninta da Mali.

Kasashen uku da ke karkashin mulkin soja sun sanar da daukar wannan matakin hadin gwiwa ne bayan Mali ta zargi sojojin Algeria da harbo wani jirginta mara matuki a sararin samaniyarta a karshen watan Maris.

A ranar 1 ga Afrilu, Algeria ta sanar cewa ta harbo wani jirgin sama mara matuki mai dauke da makamai a sararin samaniyarta, amma ba ta yi karin bayanin ba.

A cikin wata sanarwa, Ma’aikatar Harkokin Wajen Mali ta ce hukumomi sun tabbatar da “cikakken yakini” cewa an harbo jirgin ne a cikin “A matsayin harin makiya da aka shirya daga gwamnatin Algeria.”

Gobara ta kona motoci 10 a garejin Borno Express Kisan Janar Alƙali: Kotu ta ɗage shari’a zuwa 28 ga Mayu

Sanarwar ta ce an gano burbushin jirgin kilomita 9.5 kudu da iyakar Algeria kuma an harbo shi ne da “makami mai linzami.”

Da take bayyana shi a matsayin “abin da bai taba faruwa ba na cin zarafi,” sanarwar ta ce Mali “ta yi Allah wadai da kakkausan harshe game da wannan aikin makiya, rashin abokantaka, da kuma nuna girman kai daga hukumomin Algeria.”

Algeria ba ta yi wani tsokaci nan take game da janye jakadun ba, amma ta sanar a ranar Litinin cewa ta rufe sararin samaniyarta ga jiragen sama da ke zuwa ko tafiya Mali.

Ma’aikatar tsaron Algeria ta ce, “Saboda yawan keta hurumin sararin samaniyarmu da Mali ke yi, gwamnatin Algeria ta yanke shawarar rufe zirga-zirgar jiragen sama da ke zuwa ko tafiya Mali, tun daga yau.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jirgi mara matuki Nijar Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje

Lamarin ya ci gaba da raguwa har zuwa 2024, inda yawan kudaden da ake kashewa a yawon ketare ya fadi da kaso 14 a matakin shekara-shekara zuwa dala biliyan 2.66.

Hakan na nuni da cewa ‘yan Nijeriya sun rage kashe kudaden da suke kashewa kan safarar jiragen sama da dala biliyan 1.12 ko kuma kashi 30 cikin dari a cikin shekaru biyun.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  •   Iran  Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35  Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  • Babu wanda ya tsira daga hatsarin Jirgin Air India mai dauke da fasinjoji 242
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki