Aminiya:
2025-07-31@13:50:03 GMT

Mali, Nijar, da Burkina Faso sun janye jakadunsu daga Algeria

Published: 8th, April 2025 GMT

Kasashen Mali, Nijar, da Burkina Faso sun janye jakadunsu daga kasa Algeria bayan takaddamar da ta barke tsakaninta da Mali.

Kasashen uku da ke karkashin mulkin soja sun sanar da daukar wannan matakin hadin gwiwa ne bayan Mali ta zargi sojojin Algeria da harbo wani jirginta mara matuki a sararin samaniyarta a karshen watan Maris.

A ranar 1 ga Afrilu, Algeria ta sanar cewa ta harbo wani jirgin sama mara matuki mai dauke da makamai a sararin samaniyarta, amma ba ta yi karin bayanin ba.

A cikin wata sanarwa, Ma’aikatar Harkokin Wajen Mali ta ce hukumomi sun tabbatar da “cikakken yakini” cewa an harbo jirgin ne a cikin “A matsayin harin makiya da aka shirya daga gwamnatin Algeria.”

Gobara ta kona motoci 10 a garejin Borno Express Kisan Janar Alƙali: Kotu ta ɗage shari’a zuwa 28 ga Mayu

Sanarwar ta ce an gano burbushin jirgin kilomita 9.5 kudu da iyakar Algeria kuma an harbo shi ne da “makami mai linzami.”

Da take bayyana shi a matsayin “abin da bai taba faruwa ba na cin zarafi,” sanarwar ta ce Mali “ta yi Allah wadai da kakkausan harshe game da wannan aikin makiya, rashin abokantaka, da kuma nuna girman kai daga hukumomin Algeria.”

Algeria ba ta yi wani tsokaci nan take game da janye jakadun ba, amma ta sanar a ranar Litinin cewa ta rufe sararin samaniyarta ga jiragen sama da ke zuwa ko tafiya Mali.

Ma’aikatar tsaron Algeria ta ce, “Saboda yawan keta hurumin sararin samaniyarmu da Mali ke yi, gwamnatin Algeria ta yanke shawarar rufe zirga-zirgar jiragen sama da ke zuwa ko tafiya Mali, tun daga yau.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jirgi mara matuki Nijar Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta bayyana cewa, a cikin watanni shidan farko na bana, an kafa sabbin kamfanoni 30,014 na masu zuba jari daga kasashen waje a babban yankin kasar Sin, wanda ya nuna karuwar hakan da kashi 11.7 cikin dari a mizanin duk shekara.

Kazalika, bayanai sun nuna cewa, saka hannun jari daga kungiyar kasashen kudu maso gabashin Asiya ya karu da kaso 8.8 cikin dari a tsakanin lokacin.

Har ila yau, jarin da aka zuba daga kasar Switzerland ya karu da kaso 68.6, na Japan ya karu da kashi 59.1, na Birtaniya ya karu da kaso 37.6, sai kuma na Jamus da ya karu da kashi 6.3, kana wanda aka zuba daga Jamhuriyar Koriya kuma ya karu da kashi 2.7 bisa dari. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa