Aminiya:
2025-06-15@08:29:04 GMT

Mutum 2 sun rasu, 13 sun ɓace a hatsarin jirgin ruwa a Bayelsa

Published: 2nd, April 2025 GMT

Mutum biyu sun rasa rayukansu, yayin da ake ci gaba da neman wasu mutum 13 da suka ɓace yayin wani hatsarin jirgin ruwa a Jihar Bayelsa.

Hatsarin ya faru ne da yammacin ranar Talata, lokacin da jirgin ruwa ɗauke da fasinjoji ya yi karo da wani jirgin kamun kifi.

HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Galadiman Kano Muna samun galabar daƙile kwararowar baƙin haure — Jamus

Masu nutso a ruwa sun fara ƙoƙarin ceto waɗanda suka ɓace.

Bayanai sun nuna cewar wani jirgi mai suna ‘Meeting Marine’ wanda ya taso daga Anyama Ijaw zuwa Lubia da Foropa ya yi karo da jirgin kamun kifi.

Jirgin na da injin 115HP kuma wani mutum da ake kira Saturday ne yake tuƙa shi.

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan ruwa a Bayelsa, Kwamared Ogoniba Ipigansi, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa har yanzu ba a samo mutum 13 ba.

Ya ƙara da cewa matsalar rashin ingantaccen yanayin sadarwa a yankin na hana aikin ceto tafiya yadda ya kamata.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Bayelsa, DSP Musa Muhammad, ya ce ba a kai musu rahoton faruwar lamarin ba tukuna, amma sun fara bincike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bayelsa Hatsarin Jirgin Ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina

Rundunar Ƴansandan Nijeriya, tare da haɗin gwuiwar sauran hukumomin tsaro, ta samu nasarar cafke mutane biyu da ake zargi da garkuwa da mutane tare da ceto mutane 11 da aka sace a jihohin Delta da Katsina. Wannan na cikin ƙoƙarin ci gaba da yaƙi da miyagun laifuka a faɗin ƙasa.

A jihar Katsina, an daƙile wani yunƙurin garkuwa da mutane a ranar 8 ga Yuni, 2025, a hanyar Danmusa zuwa Mara Dangeza, inda jami’an haɗin gwuiwa suka yi artabu da ‘yan bindiga. Bayan musayar wuta mai tsanani, jami’an suka tilasta masu laifin guduwa da raunukan harbi tare da kuɓutar da mutum 11 da suka sace ba tare da raunuka ba.

Yanzu-yanzu: Gwamnan Delta Oborevwori Ya Fice Daga PDP Zuwa APC Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa

A jihar Delta, jami’an CP-Special Assignment sun cafke wani Abubakar Hassan, wanda ake zargin jagoran gungun masu garkuwa da mutane ne da ke aiki a jihohi da dama. Bayan gudanar da bincike, ya jagoranci jami’ai zuwa maboyarsu a dajin Ozoro, inda aka ƙwato bindigogi AK-47 guda biyu da harsasai. Hakanan, wani direba, Obi Ezekiel, ya shiga hannu yayin da aka gano bindiga ƙirar gida da alburusai a motarsa.

Babban Sufeton Ƴansanda na ƙasa, IGP Kayode Egbetokun, ya yaba da ƙwarewa da kwazon jami’an tsaro a waɗannan ayyuka, tare da jan hankali cewa rundunar zata ci gaba da gudanar da irin wadannan farmaki don tabbatar da cewa babu mafaka ga masu aikata laifi a duk faɗin Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  •   Iran  Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35  Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  • Babu wanda ya tsira daga hatsarin Jirgin Air India mai dauke da fasinjoji 242
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe