Ƙungiyar matasan Arewa ta yi Allah-wadai da jita-jitar da ake yaɗawa cewa an kashe wani ɗan ƙabilar Ibo a Jihar Kano saboda kisan wasu Hausawa mafarauta da ɓatagari suka yi kwanan a Jihar Edo.

A wani taron manema labarai da gamayyar ƙungiyoyin matasa na ƙabilu daban-daban, ta ce abin takaici ne kisan da aka yi wa Hausawa kuma tana miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Isra’ila ta kashe yara 322 cikin kwanaki 10 a Gaza — UNICEF Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha

Kazalika, ƙungiyoyin sun yaba wa Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, bisa koƙarinsa na tabbatar da zaman lafiya ya ci gaba da ɗorewa a jihar ta hanyar ɗaukar matakan gaggawa da kuma kwantar da hankalin al’ummar Kano.

Haka kuma, shugaban ƙungiyar Nworisa Micheal, ya yi watsi da zancen da ke yawo a soshiyal midiya cewa wasu matasa sun halaka wani dan ƙabilar Ibo ibo mai suna Peter Chukwudi Nwanosike, ɗan asalin garin Abagana da ke Anambra mazauni a Kano, a matsayin martani kan kisan mafarautan.

“Saɓanin abin da ake yaɗawa ba kashe shi aka yi ba, tsautsayin masu ƙwacen waya ne ya afka kuma ya yi ƙoƙarin tserewa. Babu wanda ya caka masa makami kamar yadda ake yaɗawa.”

Ƙungiyoyin sun kuma gargaɗi kafafen yaɗa labari kan illar watsa labarai ba tare da bincike ba.

Kazalika sun yaba wa Sarkin Edo kuma Enogie II, Fred Edozele Akhigbe (JP), kan fitar da sanarwar yin tir da lamarin da ya faru a Edon sa’o’i kaɗan bayan faruwarsa, da gwamnan jihar, Monday Okpebholo, kan ziyarar jajen da ya kawo Kano, da kuma ƙoƙarinsa na samar da haɗin kai da adalci kan waɗanda lamarin ya rutsa da su.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket

Wani haziƙin matashin ɗan wasan Cricket mai shekara 17 ɗan asalin ƙasar Australiya ya mutu a yau Alhamis bayan ƙwallo ta buge shi a lokacin wasa.

Ƙwallon ta bugi, Ben Austin a wuyansa ne duk da cewa yana sanye da hular kariyar kai (Helmet) a lokacin da yake ƙoƙarin kare ƙwallon da aka bugo.

Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja

Nan take aka garzaya da shi asibiti cikin mawuyacin hali, daga bisani rai ya yi halinsa.

“Mun yi matuƙar baƙin ciki da rasuwar haziƙi Ben ɗinmu, wanda ya mutu da safiyar yau Alhamis,” in ji mahaifinsa Jace Austin a cikin wata sanarwa.

A cewar jaridar ABC News, matashin ɗan wasan bai sanya rigar da ke kare wuyansa ba, hakan ne ya sa ƙwallon ta dufafe shi.

Austin ya kasance ƙwararren mai buga ƙwallo, wanda ƙungiyarsa ta Ferntree Gully Cricket Club ta ɗauke shi a matsayin “ɗan wasan Cricket mai hazaka, babban jagora kuma matashi mai ban mamaki”.

‘Yan wasa daga ƙungiyoyin biyu na India da Australia a ɓangaren mata da ke buga wasan Cricket na duniya sun sanya baƙaƙen kambu domin alhinin mutuwarsa.

Yau dai kimanin shekaru 11 rabon da wani ɗan wasan Cricket ya mutu a lokacin wasa, tun bayan da shahararren ɗan wasan nan ɗan asalin ƙasar Australia Test Phillip Hughes ya mutu a 2014.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu
  • Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati