Kisan Mafarauta: Babu wanda aka kai wa harin ramuwar gayya a Kano — Ƙungiyoyin Matasa
Published: 2nd, April 2025 GMT
Ƙungiyar matasan Arewa ta yi Allah-wadai da jita-jitar da ake yaɗawa cewa an kashe wani ɗan ƙabilar Ibo a Jihar Kano saboda kisan wasu Hausawa mafarauta da ɓatagari suka yi kwanan a Jihar Edo.
A wani taron manema labarai da gamayyar ƙungiyoyin matasa na ƙabilu daban-daban, ta ce abin takaici ne kisan da aka yi wa Hausawa kuma tana miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda lamarin ya rutsa da su.
Kazalika, ƙungiyoyin sun yaba wa Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, bisa koƙarinsa na tabbatar da zaman lafiya ya ci gaba da ɗorewa a jihar ta hanyar ɗaukar matakan gaggawa da kuma kwantar da hankalin al’ummar Kano.
Haka kuma, shugaban ƙungiyar Nworisa Micheal, ya yi watsi da zancen da ke yawo a soshiyal midiya cewa wasu matasa sun halaka wani dan ƙabilar Ibo ibo mai suna Peter Chukwudi Nwanosike, ɗan asalin garin Abagana da ke Anambra mazauni a Kano, a matsayin martani kan kisan mafarautan.
“Saɓanin abin da ake yaɗawa ba kashe shi aka yi ba, tsautsayin masu ƙwacen waya ne ya afka kuma ya yi ƙoƙarin tserewa. Babu wanda ya caka masa makami kamar yadda ake yaɗawa.”
Ƙungiyoyin sun kuma gargaɗi kafafen yaɗa labari kan illar watsa labarai ba tare da bincike ba.
Kazalika sun yaba wa Sarkin Edo kuma Enogie II, Fred Edozele Akhigbe (JP), kan fitar da sanarwar yin tir da lamarin da ya faru a Edon sa’o’i kaɗan bayan faruwarsa, da gwamnan jihar, Monday Okpebholo, kan ziyarar jajen da ya kawo Kano, da kuma ƙoƙarinsa na samar da haɗin kai da adalci kan waɗanda lamarin ya rutsa da su.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe
A yayin da ake tsaka da bikin Ranar Dimokradiyya a Najeriya, al’ummar jihar Gombe sun wayi gari da sabuwar dokar takaita zirga-zirgar babura daga ƙarfe 7:00 na yamma zuwa ƙarfe 6:00 na safe a duk faɗin jihar.
Sanarwar da ta fito ne daga hannun Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sanda ta jihar, DSP Buhari Abdullahi, ranar Alhamis, a madadin kwamishinan ’yan sandan jihar Bello Yahaya.
Sanarwar ta ce an kafa dokar ne don rage ayyukan ta’addanci a fadin jihar.
Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a FilatoKafa dokar na zuwa ne kwana uku bayan wasu matasa da ba a tantance su wane ne ba suka kashe wani magidanci mai suna Ahmad Aliyu, wanda aka fi sani da Amadi Kasiran, a unguwar Hammadu Kafi da ke Gombe, a daren Lahadi.
Sanarwar ta ƙara da cewa duk wanda aka kama ya karya dokar zai fuskanci hukunci mai tsauri, ciki har da gurfanar da shi a gaban kotu.
Kazalika, sanarwar ta ce dokar ta haramta ɗaukar mutum fiye da ɗaya a kan babur domin rage matsalar rashin tsaro a jihar.
“Dokar hana hawa babur da goyon biyu ta fara aiki ne daga yau, Alhamis, ranar bikin Dimokradiyya, har sai wani lokaci da ba a kayyade ba,” in ji Kakakin ’yan sandan.
Rundunar ’yan sandan ta ce an ɗauki wannan mataki ne don magance matsalar bata-gari na ‘’yan kalare’ da sauran ayyukan ta’addanci.
A lokacin da wakilinmu ya kai ziyara kwaryar birnin Gombe, filin wasa na Pantami ya kasance a rufe ba tare da alamar wani biki ba.
Sai dai ya gane wa idanunsa cewa an jibge jami’an tsaro a sassa daban-daban, ciki har da ’yan sanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), da kuma ’yan banga.
Wannan sabuwar doka ta ja hankalin mutane da dama a jihar, musamman mazauna yankunan da aka fi samun matsalar tsaro.
Sai dai wasu na gani za ta kara jefa jihar cikin kuncin talauci sakamakon rufe shaguna da kasuwanni da wuri saboda rashin abun hawa wanda dama can baburan aka fi hawa saboda tsadar rayuwa.