Aminiya:
2025-09-18@01:00:39 GMT

HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Galadiman Kano

Published: 2nd, April 2025 GMT

An yi jana’izar marigayi Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sunusi, a Fadar Sarkin Kano da ke Kofar Kudu, inda dubban jama’a suka halarta.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, tare da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, sun halarci jana’izar Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sunusi.

Basakkwacen da ya yi ridda ya sake karɓar addinin Musulunci Tinubu zai tafi ziyarar makonni biyu a Faransa

An gudanar da sallar jana’izar ne a Fadar Sarkin Kano da ke Kofar Kudu, inda Farfesa Sani Zahradden ya jagoranci sallar.

Dubban jama’a ne suka halarci jansiza5 marigayin.

Har ila yau, Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi II, ya halarci jana’izar.

Marigayi Alhaji Abbas Sunusi, ya rasu ne a daren ranar Talata a gidansa da ke Kano bayan doguwar jinya.

Ya rasu yana da shekara 92 a duniya.

An birne shi a makabartar Gandun Albasa.

Domin nuna alhini game da rasuwar marigayin, Gwamnatin Jihar Kano da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, sun dakatar da bukukuwan Sallar da suka shirya gudanarwa a yau Laraba.

Marigayi Galadima ya riƙe mukami mafi girma a Masarautar Kano, kuma shi ne mahaifin Abdullahi Abbas, Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Kano.

Ga hotunan yadda jana’izar ta gudana:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barau Kwankwaso masarauta rasuwa Sarkin Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

KADA ta yi gargaɗi cewa haƙurin jama’a ya ƙare, tana mai jaddada cewa shiru da halin ko-in-kula daga shugabanni ba za a ƙara yarda da shi ba. Sun yi kira da a tabbatar da adalci da kuma mayar da zaman lafiya a yankin, tare da nuna goyon baya ga iyalan mamacin da ɗaukacin al’ummar Garga.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa