Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi Allah-wadai da kakkausar murya kan hare-haren da sojojin Isra’ila suka kai kan kungiyoyin kare fararen hula da masu aikin ceto Palasdinawa a Rafah da ke kudancin zirin Gaza, tare da bayyana hakan da aikata laifukan yaki.

Sojojin Isra’ila sun amince a ranar Asabar 29 ga watan Maris cewa sun yi luguden wuta kan motocin daukar marasa lafiya a zirin Gaza, inda Hamas ta yi Allah wadai da harin” da ya janyo asarar rayukan ma’aikatan ceto.

Rahotanni sun ce an gano gawarwakin ma’aikatan ceto goma sha biyar, wadanda aka binne a kusa da motocinsu, wadanda suka lalace gaba daya sakamakon harin na Isra’ila.

Har ila yau kungiyar ta jaddada cewa kai hare-hare da gangan kan masu kai agajin da suke gudanar da ayyukansu na jin kai na nuni da daya daga cikin manyan laifukan keta dokokin yaki kuma wani bangare ne na hare-haren da gwamnatin sahyoniyawan ke ci gaba da kaiwa kan fararen hula a zirin Gaza.

Hamas ta kuma yi Allah wadai da shirun da kasashen duniya suka yi wajen fuskantar irin wadannan laifuffuka, tana mai cewa rashin daukar matakin wani abu ne da ba za a amince da shi ba.

Ma’aikatar lafiya ta gwamnatin Hamas a zirin Gaza ta fada a yau asabar cewa mutane 921 ne suka mutu a yankin tun bayan da Isra’ila ta sake kai hare-hare a ranar 18 ga Maris, ciki har da 25 a cikin sa’o’i 24 da suka gabata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

A cewarsa, ta hanyar wadannan shirye-shirye, kasar Sin ta nuna goyon baya mai dorewa ga kasashe masu tasowa kuma tana ba da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban duniya a karkashin tsarin hadin gwiwar kasashe masu tasowa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025 Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 
  • Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu
  • Jihar Jigawa Ce Ta Fara Biyan Kudaden Kujerun Aikin Hajjin 2026- NAHCON
  • Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri
  • Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati