Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello ta yi ala wadai da kisan gilla da aka yi wa ‘yan Arewa 16 a Uromi, Jihar Edo, a ranar 28 ga Maris, 2025.

 

Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda abin ya shafa suna kan hanyarsu daga Fatakwal zuwa Kano lokacin da aka kai musu farmaki, aka sare su, sannan aka banka musu wuta a abin da gidauniyar ta bayyana a matsayin abin “aikin rashin imani” na tashin hankali bisa la’akari da bambancin kabilanci.

 

A cikin wata sanarwa da Darakta-Janar na gidauniyar, Injiniya Dakta Abubakar Gambo Umar, ya fitar, gidauniyar ta nuna damuwarta kan yadda hare-haren da ake kai wa ‘yan Arewa ke ƙaruwa a wasu sassan Kudancin kasan nan, tana gargaɗin cewa irin waɗannan munanan ayyukan na barazana ga hadin kan kasa da zaman lafiya.

 

“Muna matuƙar ƙin wannan aika-aika da aka yi wa ‘yan Najeriya bisa la’akari da kabilanci da yankuna,” in ji sanarwar.

 

“Abin baƙin ciki ne cewa ‘yan ƙasa ba za su iya yin tafiye-tafiye cikin kasarsu ba cikin tsaro da kwanciyar hankali, ba tare da fargabar farmaki ko cutarwa ba.”

 

Gidauniyar ta tuna da wasu hare-haren da aka kai a baya kan ‘yan Arewa a Kudancin kasan nan.

 

“Ba zamu manta da kisan ‘yan Arewa uku a Jihar Anambra a ranar 18 ga Janairu, 2022 ba, da kisan direbobin tirela biyu a Jihar Enugu a ranar 14 ga Yuli, 2023, inda aka kona motocinsu, da kuma kisan ‘yan Arewa biyar a Jihar Delta a ranar 30 ga Oktoba, 2024,” sanarwar ta karanta.

 

“Kuma ba za mu manta da kisan gillar da aka yi wa wata mace mai ciki, Harira Jibril, da ‘ya’yanta mata guda huɗu a Jihar Ebonyi a ranar 23 ga watan Mayun 2021 ba.”

 

“Waɗannan abubuwa da makamantansu sun nuna wani yanayi mai tayar da hankali da bai kamata a yi shiru a kansa ba,” in ji gidauniyar.

 

Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Memorial ta buƙaci a gaggauta kama tare da gurfanar da masu hannu a kisan Uromi, tare da biyan diyya ga iyalan waɗanda abin ya shafa.

 

“Muna buƙatar adalci cikin gaggawa, dole ne hukumomi su hukunta waɗanda suka aikata wannan ta’asa,” sanarwar ta ci gaba.

 

Haka kuma, gidauniyar ta roƙi shugabannin Kudancin kasan nan su ɗauki matakan wayar da kan al’ummominsu don gujewa ɗora laifi bisa la’akari da kabilanci da aikata ayyukan tashin hankali.

 

“Ba kowa ne ke da ikon ɗaukar doka a hannunsa ba,” in ji ta.

 

“Allah wadai kadai ba ya isa; dole ne a yi adalci.”

 

Sanarwar ta jaddada cewa kowanne ɗan Najeriya na da ‘yancin rayuwa da aiki a kowane yanki na ƙasa, tana mai buƙatar gwamnati da ta tabbatar da kariya ga kowa ba tare da nuna bambanci ba.

 

“Idan ba mu magance irin waɗannan hare-haren ba, muna fuskantar barazanar ramuwar gayya da rarrabuwar ƙasa,” gidauniyar ta yi gargaɗi.

 

“Don ƙasarmu ta ci gaba da rayuwa cikin zaman lafiya, haɗin kai da jituwa, dole ne mu yi watsi da duk wani nau’in nuna wariya da tashin hankali.”

 

Wannan lamari ya haifar da gagarumar fusata a fadin ƙasa, tare da kiran ga gwamnati ta ɗauki matakin gaggawa domin kawo ƙarshen rikicin kabilanci da tabbatar da adalci ga waɗanda abin ya shafa.

Rel: Khadija Kubau

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa Edo Gidauniyar Jihar Yan

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

Majalisar dattawa ta dakatar da Sanata Akpoti-Uduaghan a ranar 6 ga Maris, 2025, na tsawon watanni shida. Duk da cewa an kalubalanci lamarin a kotu, amma babbar kotun tarayya ba ta bayar da wani umarni na soke dakatarwar ba ko kuma tilasta sake dawo da ita bakin aiki.

 

A ranar 4 ga Satumba, 2025, Sanatar ta sanar da ofishin magatakarda akan aniyar ta na ci gaba da ayyukan majalisa, nan take, ofishin ya mika wasikar ga shugabannin majalisar dattawan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000