Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello ta yi ala wadai da kisan gilla da aka yi wa ‘yan Arewa 16 a Uromi, Jihar Edo, a ranar 28 ga Maris, 2025.

 

Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda abin ya shafa suna kan hanyarsu daga Fatakwal zuwa Kano lokacin da aka kai musu farmaki, aka sare su, sannan aka banka musu wuta a abin da gidauniyar ta bayyana a matsayin abin “aikin rashin imani” na tashin hankali bisa la’akari da bambancin kabilanci.

 

A cikin wata sanarwa da Darakta-Janar na gidauniyar, Injiniya Dakta Abubakar Gambo Umar, ya fitar, gidauniyar ta nuna damuwarta kan yadda hare-haren da ake kai wa ‘yan Arewa ke ƙaruwa a wasu sassan Kudancin kasan nan, tana gargaɗin cewa irin waɗannan munanan ayyukan na barazana ga hadin kan kasa da zaman lafiya.

 

“Muna matuƙar ƙin wannan aika-aika da aka yi wa ‘yan Najeriya bisa la’akari da kabilanci da yankuna,” in ji sanarwar.

 

“Abin baƙin ciki ne cewa ‘yan ƙasa ba za su iya yin tafiye-tafiye cikin kasarsu ba cikin tsaro da kwanciyar hankali, ba tare da fargabar farmaki ko cutarwa ba.”

 

Gidauniyar ta tuna da wasu hare-haren da aka kai a baya kan ‘yan Arewa a Kudancin kasan nan.

 

“Ba zamu manta da kisan ‘yan Arewa uku a Jihar Anambra a ranar 18 ga Janairu, 2022 ba, da kisan direbobin tirela biyu a Jihar Enugu a ranar 14 ga Yuli, 2023, inda aka kona motocinsu, da kuma kisan ‘yan Arewa biyar a Jihar Delta a ranar 30 ga Oktoba, 2024,” sanarwar ta karanta.

 

“Kuma ba za mu manta da kisan gillar da aka yi wa wata mace mai ciki, Harira Jibril, da ‘ya’yanta mata guda huɗu a Jihar Ebonyi a ranar 23 ga watan Mayun 2021 ba.”

 

“Waɗannan abubuwa da makamantansu sun nuna wani yanayi mai tayar da hankali da bai kamata a yi shiru a kansa ba,” in ji gidauniyar.

 

Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Memorial ta buƙaci a gaggauta kama tare da gurfanar da masu hannu a kisan Uromi, tare da biyan diyya ga iyalan waɗanda abin ya shafa.

 

“Muna buƙatar adalci cikin gaggawa, dole ne hukumomi su hukunta waɗanda suka aikata wannan ta’asa,” sanarwar ta ci gaba.

 

Haka kuma, gidauniyar ta roƙi shugabannin Kudancin kasan nan su ɗauki matakan wayar da kan al’ummominsu don gujewa ɗora laifi bisa la’akari da kabilanci da aikata ayyukan tashin hankali.

 

“Ba kowa ne ke da ikon ɗaukar doka a hannunsa ba,” in ji ta.

 

“Allah wadai kadai ba ya isa; dole ne a yi adalci.”

 

Sanarwar ta jaddada cewa kowanne ɗan Najeriya na da ‘yancin rayuwa da aiki a kowane yanki na ƙasa, tana mai buƙatar gwamnati da ta tabbatar da kariya ga kowa ba tare da nuna bambanci ba.

 

“Idan ba mu magance irin waɗannan hare-haren ba, muna fuskantar barazanar ramuwar gayya da rarrabuwar ƙasa,” gidauniyar ta yi gargaɗi.

 

“Don ƙasarmu ta ci gaba da rayuwa cikin zaman lafiya, haɗin kai da jituwa, dole ne mu yi watsi da duk wani nau’in nuna wariya da tashin hankali.”

 

Wannan lamari ya haifar da gagarumar fusata a fadin ƙasa, tare da kiran ga gwamnati ta ɗauki matakin gaggawa domin kawo ƙarshen rikicin kabilanci da tabbatar da adalci ga waɗanda abin ya shafa.

Rel: Khadija Kubau

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa Edo Gidauniyar Jihar Yan

এছাড়াও পড়ুন:

Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu

George Iniobong ɗan shekara ashirin da biyu daga tawagar Jihar Binuwai ya samu kyautar azurfa a gasar maza ta Judo mai nauyin kilo 60 a yau Lahadi, yayinda ake cigaba da gasar wasanni ta ƙasa karo na 22 (NSF) da ke gudana a Abeokuta, babban birnin jihar Ogun.

Nasarar da George ya samu ya sa tawagar ta Jihar Binuwai ta samu kyautukan tagulla da Azurfa 9 jimilla a gasar, wakilinmu ya ruwaito cewa, Iniobong, ya yi matuƙar taka rawar gani a wasan inda ya samu nasara a kan abokin karawarshi daga jihar Ogun cikin mintunan ƙarshe na karawar.

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

George Iniobong yayinda yake zantawa da manema labarai bayan samun wannan gagarumar nasarar, ya yaba wa Gwamnan Jihar Binuwai, Fr. Hyacinth Alia domin abinda ya kira gudunmawar da gwamnan ya ba shi da sauran ‘yan wasa daga jihar domin su nuna bajintarsu a wasannin na Gateway wanda ya haɗa ‘yan wasa daga dukkan jihohin kasar nan 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja, domin fafatawa a wasanni daban-daban, da niyyar inganta hadin kai da kwazo a fadin Najeriya.

“Duk da cewar nayi tunanin samun kyautar zinare a wannan wasan amma ina sa ran kasancewa cikin masu samun wannan kyautar zuwa gaba, Nasara ta na tare dani da kuma jihar Binuwai” inji shi, “Duk da haka na ƙara samun ƙwarin gwuiwa da gogewa, kuma a shirye nake in bayar da duk abin da zan yi wajen samun nasarar jihar idan wata dama ta samu ya kara da cewa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato
  • Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu
  • Ndume ya jinjina wa Tinubu kan bai wa ’yan Arewa sabbin muƙamai
  • Afirka Ta Kudu Ta Zargi Shugaban Kasar Amurka Da  Rashin Dalili Akan Zargin Yi Wa Fararen Fatar Kasar Kisan Kiyashi
  • Afrika ta Kudu ta karyata ikirarin Trump na kisan kiyashin fararen fata
  • ‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu
  • Tinubu Zai Bibiyi Kwazon Ministocinsa A Ranar 29 Ga Watan Mayu
  • ‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
  • SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
  • Abin da muka sani kan labarin juyin mulki a Kwadebuwa