Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello ta yi ala wadai da kisan gilla da aka yi wa ‘yan Arewa 16 a Uromi, Jihar Edo, a ranar 28 ga Maris, 2025.

 

Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda abin ya shafa suna kan hanyarsu daga Fatakwal zuwa Kano lokacin da aka kai musu farmaki, aka sare su, sannan aka banka musu wuta a abin da gidauniyar ta bayyana a matsayin abin “aikin rashin imani” na tashin hankali bisa la’akari da bambancin kabilanci.

 

A cikin wata sanarwa da Darakta-Janar na gidauniyar, Injiniya Dakta Abubakar Gambo Umar, ya fitar, gidauniyar ta nuna damuwarta kan yadda hare-haren da ake kai wa ‘yan Arewa ke ƙaruwa a wasu sassan Kudancin kasan nan, tana gargaɗin cewa irin waɗannan munanan ayyukan na barazana ga hadin kan kasa da zaman lafiya.

 

“Muna matuƙar ƙin wannan aika-aika da aka yi wa ‘yan Najeriya bisa la’akari da kabilanci da yankuna,” in ji sanarwar.

 

“Abin baƙin ciki ne cewa ‘yan ƙasa ba za su iya yin tafiye-tafiye cikin kasarsu ba cikin tsaro da kwanciyar hankali, ba tare da fargabar farmaki ko cutarwa ba.”

 

Gidauniyar ta tuna da wasu hare-haren da aka kai a baya kan ‘yan Arewa a Kudancin kasan nan.

 

“Ba zamu manta da kisan ‘yan Arewa uku a Jihar Anambra a ranar 18 ga Janairu, 2022 ba, da kisan direbobin tirela biyu a Jihar Enugu a ranar 14 ga Yuli, 2023, inda aka kona motocinsu, da kuma kisan ‘yan Arewa biyar a Jihar Delta a ranar 30 ga Oktoba, 2024,” sanarwar ta karanta.

 

“Kuma ba za mu manta da kisan gillar da aka yi wa wata mace mai ciki, Harira Jibril, da ‘ya’yanta mata guda huɗu a Jihar Ebonyi a ranar 23 ga watan Mayun 2021 ba.”

 

“Waɗannan abubuwa da makamantansu sun nuna wani yanayi mai tayar da hankali da bai kamata a yi shiru a kansa ba,” in ji gidauniyar.

 

Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Memorial ta buƙaci a gaggauta kama tare da gurfanar da masu hannu a kisan Uromi, tare da biyan diyya ga iyalan waɗanda abin ya shafa.

 

“Muna buƙatar adalci cikin gaggawa, dole ne hukumomi su hukunta waɗanda suka aikata wannan ta’asa,” sanarwar ta ci gaba.

 

Haka kuma, gidauniyar ta roƙi shugabannin Kudancin kasan nan su ɗauki matakan wayar da kan al’ummominsu don gujewa ɗora laifi bisa la’akari da kabilanci da aikata ayyukan tashin hankali.

 

“Ba kowa ne ke da ikon ɗaukar doka a hannunsa ba,” in ji ta.

 

“Allah wadai kadai ba ya isa; dole ne a yi adalci.”

 

Sanarwar ta jaddada cewa kowanne ɗan Najeriya na da ‘yancin rayuwa da aiki a kowane yanki na ƙasa, tana mai buƙatar gwamnati da ta tabbatar da kariya ga kowa ba tare da nuna bambanci ba.

 

“Idan ba mu magance irin waɗannan hare-haren ba, muna fuskantar barazanar ramuwar gayya da rarrabuwar ƙasa,” gidauniyar ta yi gargaɗi.

 

“Don ƙasarmu ta ci gaba da rayuwa cikin zaman lafiya, haɗin kai da jituwa, dole ne mu yi watsi da duk wani nau’in nuna wariya da tashin hankali.”

 

Wannan lamari ya haifar da gagarumar fusata a fadin ƙasa, tare da kiran ga gwamnati ta ɗauki matakin gaggawa domin kawo ƙarshen rikicin kabilanci da tabbatar da adalci ga waɗanda abin ya shafa.

Rel: Khadija Kubau

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa Edo Gidauniyar Jihar Yan

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya soki Shugaban Amurka, Donald Trump, bisa kiran Najeriya “ƙasa mai matsala ta musamman” kan zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

Sani, ya ce kalaman Trump sun samo asali ne daga bayanan da ba su da tushe, da wasu mutane suka ba shi domin su tayar da fitina a Najeriya.

Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’u

A ranar Juma’a ne, Trump ya wallafa rubutu a shafinsa na sada zumunta cewar Kiristanci yana cikin hatasri a Najeriya.

Ya yi iƙirarin cewa ’yan ta’adda sun kashe dubban Kiristoci, amma ya ce Amurka za ta yi duk mai yiwuwa wajen “ceto Kiristoci” a Najeriya da wasu ƙasashe.

Shehu Sani, ya mayar da martani da cewa wannan magana ba gaskiya ba ce, domin matsalar tsaro a Najeriya ba ta da nasaba da addini.

Ya ce Musulmai da Kiristoci dukkaninsu suna fuskantar hare-haren’yan ta’adda da garkuwa da su.

“Wannan zargi ƙarya ne. ’Yan ta’adda da ’yan bindiga a Najeriya suna kashe mutane ba tare da la’akari da addininsu ba. Wannan abin na faruwa tun kusan shekaru 15 da suka wuce,” in ji shi.

Sani, ya ƙara da cewa, saboda yawan Musulmai da Kiristoci a Najeriya, ba zai yiwu addini ɗaya ya zalunci ɗaya ba.

“Idan aka duba yadda Musulmai da Kiristoci suke kusan daidai a Najeriya, ba zai yiwu ɗaya ya zalunci ɗaya ba. Najeriya kamar zaki da damisa ce, dukkanin ɓangarorin suna da ƙarfi,” in ji shi.

Ya zargi waɗanda suka zuga Trump da amfani da rikice-rikicen cikin gida na Najeriya.

“Trump ya samu bayanan ƙarya daga mutanen da ke son raba Najeriya domin su ci moriya daga wannan,” in ji shi.

“Wannan makirci da aka yi wa ƙasar nan ba zai yi nasara ba.”

Sani, ya roƙi ƙasashen duniya su taimaka wa Najeriya wajen yaƙar ta’addanci, maimakon yaɗa labaran ƙarya.

“Najeriya na buƙatar taimako da haɗin kai wajen shawo kan matsalar tsaro, kamar sauran ƙasashen da ke fama da ta’addanci,” a cewarsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai