Sojojin Sudan Suna Ci Gaba Da Samun Nasara A Akan Dakarun Kai Daukin Gaggawa
Published: 27th, March 2025 GMT
A yau Alhamis sojojin na kasar Sudan sun sanar da abinda su ka kira; Yin shara a cikin birnin Khartum, domin gano inda gyauron mayakan dakarun rundunar sa-kai suka buya.
Haka nan kuma sojojin na Sudan sun sanar da sakin farsunoni masu yawa da rundunar kai daukin gaggawa din suka tsare su, a lokacin da suke rike da birnin na Khartum.
Sojojin kasar ta Sudan sun nuna shugaban majalisar sojan kasar Janar Burhan a cikin fadar shugaban kasa, inda ya sanar da cewa; An ‘yanto da Khartum.
A karon farko jirgin Janar Burhan ya sauka a filin saukar jiragen sama na Khatrum, tun bayan da yaki ya barke.
Tun a jiya Laraba ne dai sojojin na Sudan su ka sanar da shimfida ikonta akan filin saukar jiragen sama na Khartum wanda shi ne tunga ta karshe da ta saura a hannun rundunar kai daukin gaggawa.
Kwamandan rundunar sojan Sudan da take fada a birnin na Khartum Lafatnar kasar Abdurrahman al-Bilawi ne ya sanar da cewa, an shimfida iko a cikn filin saukar jiragen sama na kasa da kasa na birnin Khartum.
Har ila yau kwamandan sojan ya kuma bayyana cewa, a yanzu haka suna cigaba da faraurar mayakin “Rundunar Kai Daukin Gaggawa”da su ka saura a cikin binin Khartum.
Kwanaki kadan da su ka gabata ne dai sojojin na Sudan su ka kwato fadar shugaban kasa wacce ta dauki shekaru biyu a hannun rundunar kai daukin gaggawa, haka nan kuma babbar cibiyar soja da tsakiyar birnin Khartum da can ne ma’aikatu da dama suke.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: rundunar kai
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
Shugaban kasar Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya fada wa Shugaban Amurka Donald Trump cewa; a Nigeria ba a lamunta da duk wani rikicin addini.
Shugaban na kasar Najeriya ta mayar wa da Tinubu martani ne saboda yadda ya bayyana Najeriya a matsayin kasa mai jawo damuwa ta musamman”, bisa zargin cewa Mabiya addinin kiristanci suna fuskantar barazanar karewa, ya kuma yi alkawalin cewa Amurkan za ta ba su kariya.
Donald Trump ya ce; Kiristoci suna fuskantar barazanar karar da su a Nigeria, an kuma kashe dubban kiristoci a kasar.”
A yau Asabar, kwana daya daga wancan zancen na Tinibu ne dai shugaban kasar ta Nigeria Bola Ahamd Tinubu mayar da martanin da ya kunshi cewa: Nageria kasa ce ta Demokradiyya, kuma tsarin mulkinta ya lamuncewa kowa ‘yancin yin addini.”
Har ila yau shugaban kasar ta Najeriya ya ce; Tun daga 2023 gwamnatinmu take mu’amala da hulda da dukkanin malaman kirista da musulmi, kuma tana ci gaba da magance matsalar tsaro da ta shafi dukkanin mutanen kasar daga kowane addini a cikin yankunan kasar.
Shugaba Tinubu ya kuma ce; Bayyana Nigeria a matsayin kasa wacce ake fada da addini, ba ya nuni da hakikanin yadda rayuwa take a kasar, kuma ba a yi la’akari da yadda gwamnati take aiki tukuru domin kare ‘yancin yin addini da akidun mutanen Nigeria ba.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci