Leadership News Hausa:
2025-09-18@03:45:40 GMT

Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya

Published: 24th, March 2025 GMT

Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya

Al’ummar duniya mai kyakkyawar makomar bai daya na nufin makomar kowace al’umma da kowace kasa tana da nasaba da juna. Hakan na nufin ya kamata mu yi rayuwa tare duk rintsi duk wuya, muna more daukaka da wahala tare da kuma kokarin mayar da duniyarmu al’umma guda mai jituwa, inda za mu mai da burin mutane na samun ingantacciyar rayuwa ta zama gaskiya.

Shekaru 12 da suka gabata, lokacin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya fara ziyarar aiki ta farko a matsayinsa na shugaban kasar Sin, ya gabatar da wannan ra’ayi mai cike da hangen nesa. Tun daga wannan lokacin, ra’ayin ko tunani ya bunkasa zuwa wani tsari na musamman da ake aiwatarwa, tare da samun kaso mafi girma na amincewa daga kasashen duniya. A yau, ba wai kawai ra’ayin ya kunshi nuna nagartattun dabi’un bai daya ba ne, har ma ya kasance shimfidar tsarin tunani na yin gyare-gyare na Majalisar Ɗinkin Duniya yayin da take cika shekaru 80 da kafuwa.

Tunanin al’ummar duniya mai kyakkyawar makomar bai daya shi ne ginshikin tunanin Xi Jinping kan harkokin diflomasiyya, wanda ke wakiltar zurfafa fahimtar kasar Sin game da muhimman dokokin dake kula da ci gaban zamantakewar dan Adam, kuma yake ba da amsa ta musamman ta Sinawa ga tambayar “Wace irin duniya ce ya kamata mu gina, kuma ta yaya za mu gina ta?” Tun farkon wannan zamani da muke ciki, wannan hangen nesa ya sauya daga shawarar kasar Sin zuwa yarjejeniya ta kasa da kasa, daga buri zuwa aiki na hakika, kuma daga faffadan ra’ayi na falsafa zuwa tsarin bayanai game da aiwatar da manufofi. Kana ya zama fayyatacciyar ka’idar zamaninmu, wanda ta shimfida hanyar hadin gwiwar duniya da gudanar da mulkinta. Har ila yau, gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makomar bai daya na nufin yunkurin samar da kyakkyawar duniya mai cike da zaman lafiya, aminci, wadata, budaddiya, hadaka, da kuma tsabta. Kazalika ra’ayin yana kira da a samar da sabon tsarin gudanar da harkokin duniya bisa tuntuba, da ba da gudunmawar hadin gwiwa, da fa’idodi na bai daya, masu daukar dabi’un da suka dace da dan Adam. Yana kuma habaka sabon nau’in alakar kasa da kasa, ta hanyar kaddamar da shirin Raya Duniya, da shirin Tsaron Duniya, da shirin Wayewar Kai na Duniya dake aiki a matsayin ginshikan wannan tunanni. Haka ma hadin gwiwa mai inganci karkashin tsarin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya mai amfani wajen aiwatar da wannan hangen nesa, tana bai wa kasashe damar yin aiki tare wajen magance kalubalen duniya da samun wadata tare. Wannan hangen nesa a karshe yana jagorantar duniya zuwa ga makoma mai cike da zaman lafiya, tsaro, wadata da ci gaba. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ummar Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin

Babban attajirin Afirka kuma Shugaban Rukunin Kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya ɗauki nauyin gina ɗakunan kwanan ɗalibai masu gadaje 250 da Babban Masallacin Juma’a na Ilorin ya tsara a Jami’ar Ilorin da ke Jihar Kwara.  

An kiyasta aikin zai ci kusan naira biliyan 1.1, kuma an ƙaddamar da shi ne domin samar da hanyar samun kuɗin kula da masallacin.

Ana sa ran kuɗaɗen haya da za a samu daga ɗaliban da za su zauna a wurin zai rika shiga asusun kula da masallacin.

Sakataren kwamitin amintattu na masallacin, Alhaji Shehu AbdulGafar, ya shaida wa manema labarai a Ilorin cewa Ɗangote ya riga ya sanar da su cewa zai ɗauki nauyin aikin gaba ɗaya.

Cire tallafin man fetur shi ne abin da ya dace —Sarki Sanusi II NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa

Ya ce an riga an rattaba hannu kan yarjejeniya da Jami’ar Ilorin wadda ta ba wa masallacin damar mallaka da gudanar da ɗakin kwanan ɗaliban na tsawon shekaru 21 kafin a miƙa shi ga jami’ar.

Baya ga aikin ginin, Ɗangote ya kuma yi alƙawarin bayar da tallafin Naira miliyan 5 a kowane wata domin kula da masallacin har sai an kammala aikin.

AbdulGafar ya ce wannan taimako zai rage nauyin kuɗin aikin, tare da tabbatar da ɗorewar ayyukan masallacin.

Ya ƙara da cewa ɗakin kwanan zai taimaka wajen rage matsalar ƙarancin wurin kwana ga ɗaliban jami’ar.

Shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki sun yaba wa Ɗangote, sun bayyana wannan mataki a matsayin abin koyi na yadda za a iya haɗa kai tsakanin cibiyoyin addini da ’yan kasuwa wajen ci-gaban al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin