Shugaba Vladimr Putin Na Kasar Rasha Ya Amince Da Tsagaita Wuta A Yakin Ukraine
Published: 13th, March 2025 GMT
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya bada sanarwan amincewa da tsagaita budewa juna wuta tsakanin Rasha da Ukraine na tsawon kwanaki 30, wanda shugaban kasar Amurka Donal Trump ya gabatar, sai dai akwai bukatar karin bayani filla-filla kan yadda hakan zai kasance. Sannan yana fadar wannan zai kai ga tsagaita budewa juna wata na din din din.
Shafin yanar Gizo na labarai Africa News ya nakalto shugaban yana fadar haka a yau Alhamis. Ya kuma kara da cewa akwai bukatar a kara tattaunawa da abokammu na kasar Amurka don kara fayyace yadda tsagaita wutan zai kasance.
Daga cikin abubuwan da za’a tattauna akwai yiyuwar sabawa yarjeniyar da kuma matakan da za’a dauka don hana hakan faruwa ko kuma idan ya faru matakan da yakamata a dauka, wa kuma zai kula da wannan bangaren.
Sannan ya kara da cewa shin kasar Ukraine zata yi amfani da wadannan kwanaki 30 don ta kara tara makamai da kuma shirin fara sabon yakin ne.
Shugaba Putin ya kara da cewa: Ya amince da tsaida yaki, da kuma fatan tsaida shi zai share hanyar samar da zaman lafiya na din din din tsakanin kasashen biyu da kuma yankin, tare da magance matsalolin da suka haddasa yakin.
Daga karshe shugaban ya godewa shugaban kasar Amurka Donal Trump saboda bada lokacinsa don kashe wutan da ke ci a kasar Ukraine fiye da shekari 3 da suka gabata.
Sannan yace kasar Rasha ba zata amince da sojojin tabbatar da zaman lafiya daga kasahsen kungiyar tsaro ta nato ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bude kofofin wuta a kan haramtacciyar kasar Isra’ila ta hanyar mayar da martani kan harin da yahudawan sahayoniyya suka kai kan kasarta
Iran ta bude kofofin jahannama kan ‘yan sahayoniyya a matsayin mayar da martani ga mummunan zaluncin da suka kaddamar kan lardunan Iran da dama, wanda ya yi sanadiyyar shahadan mutane da dama da jikkata.
Bayan da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa: Wajibi ne gwamnatin mamayar Isra’ila ta jira mummunan hukunci mai tsanani da kuma makoma mai daci kan abin da aikata, kuma bayan da sabon kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci Manjo Janar Muhammad Pakpour ya bayyana cewa: Sojojin kasar Iran za su bude kofofin jahannama kan kisan yara kanana, Iran ta fara kaddamar da hare-haren daukan fansa mai suna “Alkawarin Gaskiya na 3”, inda ta harba makamai masu linzami na ballistic da hypersonic kan yankuna daban daban na haramtacciyar kasar Isra’ila.
A cewar faifan bidiyo da aka wallafa, hakika Iran ta kai hare-hare da makamai masu linzami kan tsakiyar birnin Tel Aviv da kuma cibiyoyi da dama na soji da sansanonin sojin saman haramtacciyar kasar Isra’ila.