Leadership News Hausa:
2025-07-11@07:34:37 GMT

Halayen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (2)

Published: 8th, March 2025 GMT

Halayen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (2)

3.Mai dauriya / hakuri

Hakuri yana da matukar kyau ace kana da shi a matsayinka na Malami ka kuma nunawa dalibai domin su ta shi da shi, wadanda kamar yadda aka yi bayani cikin maganar dabarun koyarwa,suna iya daukarka, a matsayin wanda za su rika yin koyi da kai saboda su koyi halinka na hakuri.Matukar akwai hakuri za a samu saukin yin aiki tare da kowadanne matsaloli ko fadi tashin da dalibi yake yi,wanda hakan na iya zama masa babban wani tarnaki wanda zai wuyar gano bakin zaren,ko kuma abin ya zama tamkar tafiyar Kura.

4. A rika yin abubuwan jawo ankali

Dalibai suna fara koyo ne tun lokacin da suke ‘yan yara hakan kuma ne ya basu damar fadawa Malamai cewar su gaji da yadda kai Malami/ko Malamai suke koya ma su.Matukar kana son ka yi dalilin yadda ajin na ka zai zama abin burgewa,don haka idan ka gano yadda lamarin yake,sai ka yi amfani da damar wajen kawo masu misalan ra’ayoyin da za su jawo hankalinsu,har abin ya shiga zuciyarsu da kuma maida hankalinsu kan abinda ake koya masu!

5.Rika saurare sosai

Yin saurare hakan na da amfani saboda gane matsalar da bada taimakon yadda za ayi maganin abin wato su matsaolin.Ka nemi a baka irin halin da ake ciki,bada kwarin gwiwa bil hakki da gaskiya, samar da hanyoyin da dalibai za su rika tuntubar ka a saukake,ka kuma tsaida hankalinka duk lokacin da kake saurare,ko wane lokaci ka yi kokarin gane manufa lokacin da ake yin magana,ka kuma lura dakyau yadda labarin zuciya yake lokacin d a kake magana ko ake yi maka.Yi kokarin sanin me yasa d a kuma dalilin da yasa za kayi hakan

6.Mai/ Masu son abinda suke koyawa

Masana ilimi ba wai kawai suna sha’awar aikin koyarwar bane bugu da kari ma suna da sha’awa ta daukar lokaci mai tsawo suna kasancewar su ta masu koyo,wanda irin haka yana nunawa a gwagwarmayar su ta masu koyarwa. Ci gaba da koyo da bunkasar kwarewar kwararru irin hakan yana matukar taimakawa ta yadda kwararru za su kasance koda yaushe suna cikin “shirin kota kwana”da kuma tunatar da Malamai da irin matsalolin duniya mai nuna cewa dalibansu na iya fuskanta,sai kuma samar da wata dama ta nuna damuwa da abubuwan da suke damun wasu.Kara gano lamurran dangane da muhimmancin daukar lokaci mai tsawo ana koyo,da kuma yadda dabarun hanyoyin koyo za su taimaka maku ku koyar ko kuma gane/gano sababbin abubuwan da suka shafi ilimi.

7.Su zama basu da nuna bambanci

Matsayinka na mai ilimi zaka kasance da alhakin koyarda dalibai masu bambancin fahimtar ita koyarwar.Idan za ka yi maganin nuna bambanci,da kuma yin adalci,akwai bukatar ka rika gwada bukatar dalibanka,ta hanyar da babu nuna wani fifiko,abinda yake bukatar kai ka ci gaba da yin bincike da kuma bada bayani kan yadda ka fahimci ko nazarci wasu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Halaye Makaranta

এছাড়াও পড়ুন:

An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi

Wata rundunar haɗin gwiwa ta jami’an tsaro ta samu nasarar kuɓutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su da shanu da aka sace a Jihar Kebbi.

Bayanai sun ce an sace mutanen da dabbobin ne a ƙauyukan Ukuhu da Kokanawa a Karamar Hukumar Danko Wasagu ta jihar.

‘ADC za ta mayar da APC jam’iyyar adawa a 2027’ Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC

Wani daraktan tsaro a Gwamnatin Kebbi, Abdurrahama Zagga ne ya sanar wa manema labarai nasarar da aka samu a ranar Talata, inda ya ce an kai samamen ne bayan umarni da aka samu daga Gwamna Nasiru Idris bisa bayanan sirri da aka tattaro a yankin.

A cewar Zagga, tawagar jami’an tsaro ta fatattaki ’yan ta’addan da suka yi garkuwa da mutanen da kuma shanun da suka sace a wani gulbi da ke iyaka da Jihar Zamfara.

“Mutane da aka ceto an mika su ga iyalansu. Kuma wannan abin farin ciki ne ga gwamna musamman a kokarin da jami’an tsaro suke yi, lamarin da zai kara inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin masarautar Zuru.”

Ya bayyana fatan da suke da shi na kawar da ɓarayin shanu da ’yan bindigar Lukurawa a yankin Zuru da Argungu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Muna so a kafa doka ta bincikar yadda ’yan Nijeriya ke tara dukiya — EFCC
  •  Masu Kare Hakkin Dan’adam Suna Allawadai Da Takunkumin Amurka  Akann Jami’ar MDD A Falasdinu
  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • Tinubu ne ya buɗe wa Buhari ƙofar zama shugaban ƙasa — Hadimi
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata
  • Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
  • Hukumar EFCC Ta Kai Wa Yaran Makaranta Yaki Da Rashawa A Ilorin
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikaciyar ofishin jakadancin Ghana a Abuja
  • Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense
  • An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi