Leadership News Hausa:
2025-06-15@08:12:34 GMT

Halayen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (2)

Published: 8th, March 2025 GMT

Halayen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (2)

3.Mai dauriya / hakuri

Hakuri yana da matukar kyau ace kana da shi a matsayinka na Malami ka kuma nunawa dalibai domin su ta shi da shi, wadanda kamar yadda aka yi bayani cikin maganar dabarun koyarwa,suna iya daukarka, a matsayin wanda za su rika yin koyi da kai saboda su koyi halinka na hakuri.Matukar akwai hakuri za a samu saukin yin aiki tare da kowadanne matsaloli ko fadi tashin da dalibi yake yi,wanda hakan na iya zama masa babban wani tarnaki wanda zai wuyar gano bakin zaren,ko kuma abin ya zama tamkar tafiyar Kura.

4. A rika yin abubuwan jawo ankali

Dalibai suna fara koyo ne tun lokacin da suke ‘yan yara hakan kuma ne ya basu damar fadawa Malamai cewar su gaji da yadda kai Malami/ko Malamai suke koya ma su.Matukar kana son ka yi dalilin yadda ajin na ka zai zama abin burgewa,don haka idan ka gano yadda lamarin yake,sai ka yi amfani da damar wajen kawo masu misalan ra’ayoyin da za su jawo hankalinsu,har abin ya shiga zuciyarsu da kuma maida hankalinsu kan abinda ake koya masu!

5.Rika saurare sosai

Yin saurare hakan na da amfani saboda gane matsalar da bada taimakon yadda za ayi maganin abin wato su matsaolin.Ka nemi a baka irin halin da ake ciki,bada kwarin gwiwa bil hakki da gaskiya, samar da hanyoyin da dalibai za su rika tuntubar ka a saukake,ka kuma tsaida hankalinka duk lokacin da kake saurare,ko wane lokaci ka yi kokarin gane manufa lokacin da ake yin magana,ka kuma lura dakyau yadda labarin zuciya yake lokacin d a kake magana ko ake yi maka.Yi kokarin sanin me yasa d a kuma dalilin da yasa za kayi hakan

6.Mai/ Masu son abinda suke koyawa

Masana ilimi ba wai kawai suna sha’awar aikin koyarwar bane bugu da kari ma suna da sha’awa ta daukar lokaci mai tsawo suna kasancewar su ta masu koyo,wanda irin haka yana nunawa a gwagwarmayar su ta masu koyarwa. Ci gaba da koyo da bunkasar kwarewar kwararru irin hakan yana matukar taimakawa ta yadda kwararru za su kasance koda yaushe suna cikin “shirin kota kwana”da kuma tunatar da Malamai da irin matsalolin duniya mai nuna cewa dalibansu na iya fuskanta,sai kuma samar da wata dama ta nuna damuwa da abubuwan da suke damun wasu.Kara gano lamurran dangane da muhimmancin daukar lokaci mai tsawo ana koyo,da kuma yadda dabarun hanyoyin koyo za su taimaka maku ku koyar ko kuma gane/gano sababbin abubuwan da suka shafi ilimi.

7.Su zama basu da nuna bambanci

Matsayinka na mai ilimi zaka kasance da alhakin koyarda dalibai masu bambancin fahimtar ita koyarwar.Idan za ka yi maganin nuna bambanci,da kuma yin adalci,akwai bukatar ka rika gwada bukatar dalibanka,ta hanyar da babu nuna wani fifiko,abinda yake bukatar kai ka ci gaba da yin bincike da kuma bada bayani kan yadda ka fahimci ko nazarci wasu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Halaye Makaranta

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi

A cewarsa, dukkanin takardar neman kirkirar sabon masarauta ko sarki ko gunduma dole ne a aike zuwa addireshin gwamnan jihar ta hannun babbar sakatariyar ma’aikatar kananan hukumomi da kula da masarautu na jihar.

Kazalika, ya ce dole ne masu nema su gabatar da takaitaccen tarihin al’ummar da suke nema wa masarauta ko sarki ko gudunmawa tare da tarihin masarautar ko sarki ko gundumar da ke yankin da suke neman fita daga ciki.

Sanarwar ta kuma nemi a sanya dukkanin wani muhimmin bayanin da aka san zai iya taimakawa wajen la’akari da bukatar masu nema.

Har ila yau, sanarwar ta ce dole ne a takardar neman a samu sahihin sanya hannun hakimi, sarakunam kauye, da shugabannin al’umma tare da tabbacin wannan neman ta fito ne daga al’ummar wannan yankin da ake nema mata masarauta ko sarki ko gunduma.

Sanarwar ta kara da cewa duk al’ummomin da ke son kirkirar sabbin masarautu, sarakuna, ko gundumomi su na da dama kuma su na da ‘yancin gabatar da bukatar neman.

Gidado ya jaddada cewa shirin na daya daga cikin kudirin gwamnati na bunkasa gudanar da harkokin kananan hukumomi, da kiyaye al’adu, da karfafa cibiyoyin gargajiya a matsayin muhimman ginshikan zaman lafiya, hadin kai, da ci gaba masu ma’ana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi
  • Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49