A cikin abubuwan da aka tattauna a taron, a cikin kananan hukumomi 774, Jihar Delta ce kadai mai kananan hukumomi 25, suka mika bayanan asusunsu domin biyansu kai tsaye.

“Kawo yanzu kananan hukumomin Jihar Delta ne kawai suka bayar da bayanan asusunsu.

“Duk da haka, ana ci gaba da tuntubar babban lauyan gwamnatin tarayya game da yadda ake gabatar da asusun.

Da take maida jawabi kan kalubalen, Madein ta ce an tsara tsarin da za a aiwatar, amma kalubalen farko shi ne na tantance shugabannin kananan hukumomin da tsarin mulki ya zaba.

Ta bayyana cewa wannan matakin ya kasance mara tabbas.

“Bugu da kari, ga wadanda ke da zababben shugabanci, akwai alaman tambaya cewa wasu hanyoyin za a bi don tabbatar da cewa sun sami kasosu kai tsaye. Wannan ya faru ne saboda abubuwa da yawa na bukatar a magance su,” in ji ta.

Idan za a iya tunawa dai, Babban Bankin Nijeriya ya fara bayyana shugabanni da masu sa hannun a asusun bankuna na kananan hukumomi 774 da ke kasar a wani mataki na fara cin gashin kan kananan hukumomi.

Daraktan kula da harkokin shari’a na Babban Bankin Nijeriya, Kofo Salam-Alada, a cikin wata sanarwa ya bayyana cewa hakan ya zama dole domin tabbatar da bin diddigin kudade.

“Wannan duk na cikin tsari sanin abokin hulda. Duk wanda zai zama mai sa hannu a asusun dole ne a bayyana shi.

“Tsarin yana ci gaba, kuma muna hadin gwiwa da ofishin akanta janar. Mun kuma rubuta wa kananan hukumomin,” inj i shi.

Sai dai kungiyar shugabnnin kananan hukumomin Nijeriya ta ce ba ta samu wata sanarwa daga babban bankin kasar ba dangane da bude asusun ajiyar banki.

Idan za a iya tunawa, a ranar 11 ga Yuli, 2024, Kotun Koli ta tabbatar da ikon cin gashin kananan hukumomi 774 da ke kasar nan tare da haramta wa gwamnoni ci gaba da kula da kudaden da aka ware wa kananan hukumomi.

Kotun kolin ta kuma umurci Akanta Janar na Tarayya da ta biya kudaden kananan hukumomi kai tsaye zuwa asusunsu, inda ta bayyana rashin fitar da kudaden da jihohi 36 suka yi ya saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Amma watanni takwas bayan yanke hukuncin, har yanzu ba a fara aiki da hukuncin cin gashin kan kananan hukumomi ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnati Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa

Yayin da damina ke ƙara ƙaratowa, Gwamnatin Jihar Kano, ta fara wani aikin tsaftace manyan magudanan ruwa domin daƙile aukuwar ambaliyar ruwa.

An fara aikin ne a yankin shataletalen Baban Gwari, ɗaya daga cikin wuraren da ambaliya ke yawan aukuwa a Birnin Kano.

Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya

Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ce ke jagorantar aikin tsaftace magudanan ruwan.

Wannan mataki na daga cikin shirin gwamnatin jihar na kare rayuka, dukiyoyi, da kuma inganta ababen more rayuwa.

A lokacin ƙaddamar da aikin, Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Hashim Muhammad Dahiru, ya bayyana cewa an zaɓi Baban Gwari saboda muhimmancinsa da kuma yadda wajen yake a lokacin damina.

Ya ce wajen ya daɗe da zama wajen zubar da shara barkatai da kuma toshe hanyoyin ruwa.

Ya ƙara da cewa wannan wajen ba wai kawai muhimmiyar mahaɗa ba ce, amma kuma yana ɗaya daga cikin manyan hanyoyin ruwa da ke da alaƙa da ruwan Jakara da Kwarin Gogau.

Kwamishinan ya bayyana cewa mazauna yankin da masu wucewa sun sha fuskantar ambaliya da ta shafi rayuwarsu, lafiyarsu da kuma zirga-zirgarsu.

Ya ce wannan aikin ba na al’ada ba ce, illa alama ce da ke nuna cewa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin kare muhalli da kuma samar da birni mai jure sauyin yanayi da ambaliya.

Ya yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jagoranci da goyon bayan da ya bai wa ma’aikatar wajen aiwatar da wannan aiki.

Ya ce gwamnatin ta amince da sanya tsaftace magudanan ruwa a matsayin aikin da za a riƙa gudanarwa a kowace shekara domin tabbatar da tsaftar hanyoyin ruwa a faɗin jihar.

Haka kuma, gwamnatin ta bayar da kwangilar gyaran shataletalen Baban Gwari domin inganta zirga-zirga da rage yawan ambaliya, ta hanyar gina sabbin hanyoyin ruwa.

Kwamishinan ya bayyana cewa waɗannan matakai suna nuna irin hangen nesa da damuwar gwamnan jihar kan lafiyar jama’a da kuma kare su daga illolin da ke zuwa da ambaliya da sauyin yanayi.

Ya buƙaci jama’a da su daina zubar da shara barkatai, musamman a cikin magudanan ruwa, ya kuma buƙaci su riƙa ɗaukar nauyin tsaftace muhallinsu.

Ya ce gwamnatin za ta yi nata aikin, amma ana buƙatar haɗin gwiwar kowa da kowa domin a cimma nasara.

Ya kuma buƙaci ma’aikata da abokan aikin muhalli da su gudanar da aikinsu da kulawa da gaskiya, yana mai cewa aikin ba wai tsaftace magudanan ruwa ba ne kawai, amma aikin ne na kare rayuka, daƙile haɗura da kuma gina sabuwar Kano mai tsafta da lafiya.

A ’yan shekarun nan, yankin Baban Gwari ya yi ƙaurin suna wajen yawan aukuwar ambaliya, har ma da rasa rayuka da dukiyoyi.

Wannan ya sa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin gaggawa domin magance matsalar kafin saukar daminar bana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza