Aminiya:
2025-06-25@03:32:50 GMT

Majalisar wakilai na shirin ƙwace rajistar jam’iyyu daga hannun INEC

Published: 7th, March 2025 GMT

Majalisar Wakilai na shirin kafa wata sabuwar hukuma da za ta karɓi ikon yin rajistar jam’iyyun siyasa daga Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

Wannan na zuwa ne bayan da majalisar ta gabatar da wani sabon ƙudiri kan batun.

Sojoji sun hallaka mai haɗa wa Boko Haram bam a Sambisa Dakatarwa: Har yanzu ni Sanata ce — Natasha

Kakakin Majalisar, Hon.

Tajudeen Abbas, tare da Hon. Marcus Onobun daga Jihar Edo ne, suka gabatar da ƙudirin.

Ƙudirin na neman kafa wata hukuma mai zaman kanta da za ta riƙa yi wa jam’iyyu rajista, kula da dokokinsu, da kuma tallafa musu.

Har ila yau, ƙudirin na neman a kafa wata kotu ta musamman da za ta duba ƙorafe-ƙorafen da suka shafi jam’iyyu da rikice-rikicen da ke tasowa a tsakaninsu.

A cewar Hon. Marcus Onobun, wannan matakin ya zama dole domin kawo ƙarshen rikice-rikicen cikin gida da ke addabar jam’iyyun siyasa a Najeriya.

A halin yanzu, ƙudirin ya tsallake karatu na biyu a majalisar, lamarin da ke nuni da cewa ana iya ci gaba da duba yiwuwar aiwatar da shi a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jam iyyu Majalisar Wakilai rajista Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya bayyana matukar damuwar da Sin ke da ita dangane yanayin da yankin Gabas ta Tsakiya ke ciki, tare da bayyana fatan ganin an tsagaita bude wuta tsakanin Isra’ila da Iran nan bada jimawa ba.

Guo Jiakun ya bayyana haka ne yayin taron manema labarai na yau Talata, lokacin da yake tsokaci game da rahotannin dake cewa shugaban Amurka Donald Trump, ya sanar da cewa an cimma cikakkiyar yarjejeniyar tsagaita bude wuta tsakanin Isra’ila da Iran.

Kakakin ya kuma nanata cewa shaidu sun riga sun nuna cewa, matakan soji ba za su kawo zaman lafiya mai dorewa ba, kuma yarjejeniya da tattaunawa su ne kadai hanyoyin warware rikice-rikice.

Ya kara da cewa, Sin na kira ga bangarori masu ruwa da tsaki su bi tafarkin da ya dace na warware matsalar a siyasance nan bada jimawa ba. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
  • Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta
  • Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6
  • Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram
  • Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
  • NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu
  • Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya
  • NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin
  • Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — Rasha
  • Mutum 2 sun mutum a ƙoƙarin ciro wata daga masai a Kano