Tawagar Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ta Kare Matakin Sayar Da Jirgin Samanta Mara Mataki Ciki
Published: 23rd, February 2025 GMT
Tawagar Iran a Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa: Ba a hana sayar da jirgin mara matuki ciki na ‘Shahed’ ba
Tawagar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya ta mayar da martani kan baje kolin jirgin saman Iran a babban taron jam’iyyar Republican inda ta ce: Babu wata doka da ta haramta sayar da jirgin sama maras matuki ciki na Shahed.
Jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya kara da cewa: Jirgin sama mara matuki ciki na Shahed yana daya daga cikin mafi kyawun nau’ikan jiragen sama marasa matuka ciki a duniya, kasancewar yana da kwarewa sosai wajen ganowa, sa ido da kuma aiwatar da aiki inda ya dace, sannan kuma yana da araha da rahusa.
Jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya ci gaba da cewa: Babu wani haramcin sayar da jirgin a doka, kuma duk wata kasa da ta yi alkawarin ba za ta yi amfani da shi ba wajen kai wa wata kasa hari, tana iya neman sayan jirgin.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Iran a Majalisar Dinkin Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Yi Tir Da Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Dorawa Ma’aikaciyar MDD
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Bakai yayi tir da gwamnatin Amurka kan takunkuman da ta dorawa Francesca Albanese jami’a Ta musamman a hukumar kare hakkin bil’adama ta MDD wacce take aikin tattara bayanai dangane da yakin da ke faruwa a Gaza.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Bakaei yana fadar haka a shafinsa na X ya kuma kara da cewa ; Ba wanda ya isa ya rufe bakin gaskiya. Ya ce gwamnatin kasar Amurka ta dorawa malama Francesca Albanese takunkumi ne saboda fadin gaskiya. Saboda tsayawa kan cewa Natanyahu yana aikata kisan kiya shi a gaza. Ya na kashe yara kanan da mata. Kuma ta sha bada shawarwari ga hukumar kare hakkin bil’adama na MDD na a kori HKI daga hukumar.