Aminiya:
2025-11-02@17:15:42 GMT

Ko Real Madrid za ta iya lashe Gasar Zakarun Turai bana?

Published: 22nd, February 2025 GMT

A jiya Juma’a ce aka fitar da jadawalin zagayen ’yan 16 na Gasar Zakarun Turai ta bana a birnin Nyon.

Hukumar Ƙwallon Ƙafar Turai, UEFA, ta tsara yadda zagayen na ‘yan 16 da zagayen dab da na kusa da na ƙarshe da zagayen dab da ƙarshe da kuma zagayen ƙarshe za su kasance.

Haɗarin mota ya laƙume rayuka 12 a Neja Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano ta raba kayan tallafi

Za a kece raini ne a karawar farko ta zagayen ’yan 16 a ranakun 4 da 5 na watan Maris, inda za a yi karon-batta a karawa ta biyu bayan mako guda.

Mai riƙe da kambun gasar Real Madrid za ta kara da abokiyar hamayyarta na birni Atletico Madrid a maimaicin fafatawar ƙarshe na shekarun 2014 da 2016, waɗanda dukkaninsu Los Blancos ce ta samu galaba.

Liverpool za ta kece raini da takwararta Paris Saint-Germain a ɗaya daga cikin fafatawar da za su ɗauki hankali.

Bayern Munich za ta haɗu da abokiyar hamayyarta ta kasar Jamus Bayer Leverkusen, yayin da Arsenal za ta kara da PSV Eindhoven sannan Inter Milan za ta tunkari Feyenoord.

Barcelona za ta barje gumi da Benfica yayin da aston villa za ta hadu da Brugge, ita kuwa Borussia Dortmund za ta hadu da kungiyar Lille ta kasar Faransa.

Madrid wadda ta shiga cikin sahun masu neman gurbin zuwa zagayen ’yan 16 a kakar bana, ta yi waje rod da Manchester City wajen cimma wannan nasara.

Real Madrid ta sake doke Manchester City da ci 3 da 1 a filin wasa na Bernabeu, jimilla 6-2 a karawar da suka yi kashi biyu — gida da waje.

Madrid ta ce karɓi baƙuncin Manchester City a wasan karawa ta biyu bayan doke ta a gida (Etihad) da ci 3 da 2.

Ko a bara dai Real Madrid ce ta lashe gasar karo na 15 kuma mafi bajinta la’akari da cewa mataki ne da ba a taɓa samun wata ƙungiya ta yi makamancinsa ba a tarihi.

A karawar ƙarshe da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Borussia Dortmundta Jamus a filin wasa na Wembley, Real Madrid ta lallasa Jamusawan da ci 2-0.

Godiya ga ɗan wasan bayan Real Madrid, Dani Carvajal wanda shi ne ya yi kukan kura ya fara zura wa Dortmund ƙwallon farko a mintuna na 74 yayin da ɗan wasa Vinicius Junior shi ma ya gwada sa’arsa ya zura wa ƙungiyar ƙwallon ƙafar Jamus ɗin ƙwallo ta biyu a yayin da ake mintuna 83 da fara wasan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gasar Zakarun Turai

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugaba Samia Suluhu Hassan, wadda ke neman wa’adin ta na farko a hukumance bayan ta gaji marigayi John Pombe Magufuli a 2021, ta tsaya takara ƙarƙashin jam’iyyar CCM mai mulki. Sai dai rashin shigar manyan ‘yan adawa da aka hana tsayawa ko aka daure ya jefa shakku kan ingancin zaɓen da aka gudanar, inda masu zanga-zanga suka yi kira da a kafa gwamnatin riƙon ƙwarya da zai shirya sahihin zaɓe a gaba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3 November 1, 2025 Manyan Labarai Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa November 1, 2025 Manyan Labarai Jerin Gwarazan Taurarinmu November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano Spalleti
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
  • Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu