Aminiya:
2025-09-18@00:39:15 GMT

Ko Real Madrid za ta iya lashe Gasar Zakarun Turai bana?

Published: 22nd, February 2025 GMT

A jiya Juma’a ce aka fitar da jadawalin zagayen ’yan 16 na Gasar Zakarun Turai ta bana a birnin Nyon.

Hukumar Ƙwallon Ƙafar Turai, UEFA, ta tsara yadda zagayen na ‘yan 16 da zagayen dab da na kusa da na ƙarshe da zagayen dab da ƙarshe da kuma zagayen ƙarshe za su kasance.

Haɗarin mota ya laƙume rayuka 12 a Neja Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano ta raba kayan tallafi

Za a kece raini ne a karawar farko ta zagayen ’yan 16 a ranakun 4 da 5 na watan Maris, inda za a yi karon-batta a karawa ta biyu bayan mako guda.

Mai riƙe da kambun gasar Real Madrid za ta kara da abokiyar hamayyarta na birni Atletico Madrid a maimaicin fafatawar ƙarshe na shekarun 2014 da 2016, waɗanda dukkaninsu Los Blancos ce ta samu galaba.

Liverpool za ta kece raini da takwararta Paris Saint-Germain a ɗaya daga cikin fafatawar da za su ɗauki hankali.

Bayern Munich za ta haɗu da abokiyar hamayyarta ta kasar Jamus Bayer Leverkusen, yayin da Arsenal za ta kara da PSV Eindhoven sannan Inter Milan za ta tunkari Feyenoord.

Barcelona za ta barje gumi da Benfica yayin da aston villa za ta hadu da Brugge, ita kuwa Borussia Dortmund za ta hadu da kungiyar Lille ta kasar Faransa.

Madrid wadda ta shiga cikin sahun masu neman gurbin zuwa zagayen ’yan 16 a kakar bana, ta yi waje rod da Manchester City wajen cimma wannan nasara.

Real Madrid ta sake doke Manchester City da ci 3 da 1 a filin wasa na Bernabeu, jimilla 6-2 a karawar da suka yi kashi biyu — gida da waje.

Madrid ta ce karɓi baƙuncin Manchester City a wasan karawa ta biyu bayan doke ta a gida (Etihad) da ci 3 da 2.

Ko a bara dai Real Madrid ce ta lashe gasar karo na 15 kuma mafi bajinta la’akari da cewa mataki ne da ba a taɓa samun wata ƙungiya ta yi makamancinsa ba a tarihi.

A karawar ƙarshe da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Borussia Dortmundta Jamus a filin wasa na Wembley, Real Madrid ta lallasa Jamusawan da ci 2-0.

Godiya ga ɗan wasan bayan Real Madrid, Dani Carvajal wanda shi ne ya yi kukan kura ya fara zura wa Dortmund ƙwallon farko a mintuna na 74 yayin da ɗan wasa Vinicius Junior shi ma ya gwada sa’arsa ya zura wa ƙungiyar ƙwallon ƙafar Jamus ɗin ƙwallo ta biyu a yayin da ake mintuna 83 da fara wasan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gasar Zakarun Turai

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi

Wasu mutum shida sun shiga hannun ’yan sanda kan zargin satar zinari da kuɗinta ya haura Naira miliyan 109.5 a Jihar Kebbi.

Sashen binciken manyan laifuka na rundunar ’yan sanda a jihar Kebbi na tuhumar su da sace sarkoƙin zinare guda biyar sauran kayan zinare daga wani gida a garin Ka’oje, Ƙaramar Hukumar Bagudo.

Sauran sun haɗa da zobba huɗu da munduwar hannu tara, da nauyinsu ya kai gram 782.7 — dukkansu mallakar ’ya’ya da ’yan uwar mai gidan.

Wanda ake tuhuma ya amsa laifi

Bayan samun koken, jami’an suka kama Ibrahim Abubakar Ka’oje, jami’i a Hukumar Gyaran Hali ta Kasa, wanda a yayin bincike, ya amsa laifin.

’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu

Ya bayyana cewa ya sayar da kayan ga wasu mutane biyu, dukkansu daga Sakkwato, tare da wasu mutum biyu a Jihar Kebbi.

An kuma gano wanda  ya taimaka masa wajen sayar da wasu daga cikin kayan, inda ya karɓi naira miliyan 2.5 a matsayin lada.

Rundunar ’yan sanda ta bayyana cewa har yanzu tana neman sauran da suka gudu, bisa zargin taimakawa wajen sayar da kayan sata.

Ana zargin an sayi filaye biyu a Birnin Kebbi da kuɗin da aka samu daga sayar da kayan.

Abubuwan da aka ƙwato

Kayan da aka ƙwato sun haɗa da munduwar hannu biyu, babur ɗin Haouje, da kuma wayoyin iPhone 16, Samsung Galaxy Ultra da Samsung Flip.

Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Kebbi, Bello M. Sani, ya jinjina wa jajircewar jami’ansa bisa wannan nasara.

Ya kuma yi kira gare su da su ci gaba da aiki tukuru domin cafke sauran da ake nema da kuma ƙwato dukkan kayan da suka rage.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Hukumar Tarayyar Turai Ta Gabatar Da Shawarar Jingine Aiki Da Yarjejeniyar KAsuwanci Da HKI
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar
  • Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff