Majalisa ta tsayar da ranar sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin Dokar Haraji
Published: 19th, February 2025 GMT
Majalisar Wakilai ta sanya Laraba, 26 ga watan Fabrairu, a matsayin ranar da za ta buɗe zauren sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin dokokin haraji.
Kakakin Majalisar, Abbas Tajudeen wanda ya bayyana hakan a ranar Talata, ya ce za a gudanar da sauraron ra’ayin jama’ar a zauren majalisar na wucin-gadi.
Abba ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaro ta Kano Za a binciki INEC kan jinkirin gudanar da zaɓen cike giɓiYa bayyana cewa, kwamitin majalisar kan harkokin kuɗi ne zai jagoranci zaman sauraron ra’ayin jama’ar haɗi da wasu ƙusoshin majalisar na wasu kwamitocin.
Aminiya ta ruwaito cewa, a makon jiya ne ƙudirin kafa dokokin harajin guda huɗu da Shugaba Bola Tinubu ya aike wa majalisar suka tsallake karatu na biyu.
Wannan zaman sauraron ra’ayin da za a gudanar zai ba da damar karɓar shawarwarin masu ruwa da tsaki domin ji daga gare su dangane da ƙudirin Dokar Harajin da aka riƙa kai ruwa na a kai a faɗin ƙasar.
Idan ba a manta ba, a farkon watan Janairun da ya gabata ne gwamnonin Nijeriya suka fitar da sabon tsari na rabon haraji a ƙasar, bayan wata ganawa da suka yi da kwamitin da aka kafa domin yin nazari kan ƙudurin sabuwar dokar haraji ta ƙasar.
Tun a ƙarshen shekarar da gabata ce Tinubu ne ya gabatar wa Majalisar Tarayyar ƙudurin aiwatar da gyaran fuska ga dokar harajin, lamarin da ya haifar da zazzafar muhawara da raba kawunan shugabanni a ƙasar.
Haka ne ya kai ga cewa shugaba Tinubu da Majalisar Dokokin Tarayya sun jingine batun muhawara da amincewa da dokar har sai bayan an sake yin nazari a kanta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Haraji Majalisar Wakilai Ra ayin jama a
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta ba da shawarar a soke ko kara inganta aikin titin gina hanya mai tsawon kilomita biyar a karamar hukumar Gabasawa.
Wannan mataki ya biyo bayan karɓar rahoton da Kwamitin Majalisar kan Harkokin Jinƙai da Rage Talauci ya gabatar dangane da ambaliyar da ta afku a Zakirai, cikin karamar hukumar ta Gabasawa.
Da yake gabatar da rahoton, Shugaban Kwamitin, Alhaji Sule Lawan Shuwaki, ya bayyana wasu muhimman shawarwari da suka hada da: Umurtar kamfanin da ke aikin gina hanyar da ya faɗaɗa magudanar ruwa a yankin da abin ya shafa da kuma gaggauta kai agajin gaggawa ga waɗanda ambaliyar ta shafa.
Sauran shawarwarin sun haɗa da tura tawagar ƙwararru daga ma’aikatun ayyuka da muhalli na jihar don gudanar da bincike da bayar da shawarwarin fasaha.
Bayan nazari da tattaunawa mai zurfi, majalisar ta amince da rahoton baki ɗaya tare da kiran gwamnatin jihar da ta gaggauta ɗaukar mataki domin rage tasirin ambaliya a Zakirai.
A wani sabon lamari kuma, majalisar ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta gaggauta sake gina hanyar da ke haɗa Kwanar ‘Yan Mota zuwa Kwanar Bakin Zuwo zuwa Jakara, zuwa Kwanar Gabari a cikin karamar hukumar birnin Kano.
Wanda ya gabatar da kudirin, Honarabul Aliyu Yusuf Daneji, mai wakiltar mazabar Kano Municipal, ya jaddada cewa hanyar, musamman a kusa da kasuwar Kurmi, tana cikin matsanancin hali wanda ke kawo cikas ga zirga-zirga da kuma lalata harkokin kasuwanci.
Haka kuma, Alhaji Abdullahi Yahaya, mai wakiltar mazabar Gezawa, ya gabatar da kudiri na buƙatar gina titin kwalta daga Jogana zuwa Matallawa, Yamadi Charo da Daraudau.
Ya ce hanyar ba ta dadin bi a lokacin damina, inda al’ummar yankin ke ɗaukar matakin kansu ta hanyar cike ramuka da yashi da itace.
Kudirin ya samu goyon bayan Jagoran Masu Rinji a Majalisar, Alhaji Zakariyya Abdullahi Nuhu, tare da cikakken goyon bayan ‘yan majalisar baki ɗaya.
Sauran kudirori da aka amince da su a zaman sun haɗa da: Gina titi daga Dalawada zuwa Gazobi a karamar hukumar Tudun Wada da kuma sake gina hanyar Fanisau a Ungogo.
Daga Khadijah Aliyu