HausaTv:
2025-09-18@00:57:42 GMT

Pezeshkian : Iran Za Ta Dakile Duk Makircin Makiya

Published: 11th, February 2025 GMT

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta yi kokarin dakile duk wani makirce-makircen da makiya ke kitsawa.

Shugaban na Iran ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga dimbin jama’a da suka halarci bikin cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a shekara ta 1979 a birnin Tehran yau Litinin.

Shugaba Pezeshkian Ya soki ikirarin shugaban Amurka Donald Trump na baya-bayan nan na cewa yana son tattaunawa da Iran yayin da a lokaci guda ya ba da umarnin kakaba wa Iran takunkumi kan man da take fitarwa zuwa sifiri.”

Trump ya yi ikirarin cewa Iran na kawo cikas ga tsaron yankin amma “Isra’ila ce, tare da goyon bayan Amurka, tushen duk wani rashin tsaro a yankin da jefa kisan kiyashi a Gaza, hare-hare a kasashen Lebanon, Siriya, Iran da kuma duk inda ta ga dama.”

Pezeshkian ya yi gargadin cewa makiya suna neman haifar da fitina a cikin Iran, Sai dai kuma ba su san cewa a karkashin jagorancin Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei da kuma irin sadaukarwar da al’ummar Iran suke yi, za’a kawo karshen duk wannan mafarki.

Shugaban na Iran ya kara da cewa, Iran ba ta taba neman kaddamar da yaki kan wata kasa ba, kuma ba za ta taba mika wuya ga makiya ba.

Iran ba za ta taba barin makiya su aiwatar da munanan manufofinsu ba, in ji shugaba Pezeshkian.

Ya nanata kudurin Iran na samun zaman lafiya tare da makwabtanta bisa ‘yan uwantaka da mutunta juna, game da batun Gaza kuma, muna kare wadanda ake zalunta ne inji shi.  

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi

Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Saudiyya na iya taka muhimmiyar rawa wajen hadin kan kasashen musulmi

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Gwamnatin sahayoniyya ba za ta kuskura ta kai hari ko kai wa wata kasa ta Musulunci hari ba matukar kasashen musulmi suka hade kansu; kuma Saudiyya za ta iya taka muhimmiyar rawa a tafarkin hadin kan kasashen musulmi.

A yayin ganawarsa da yarima mai jiran gado na Saudiyya Mohammed bin Salman a gefen taron Doha, Pezeshkian ya bayyana jin dadinsa da yadda dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ke kara bunkasa, yana mai cewa: Zurfafa da karfafa hadin gwiwar dake tsakanin kasashen Iran da Saudiyya zai kare muradun kasashen biyu, da kuma muradun al’ummomin kasashen biyu, da kuma moriyar al’ummomin kasashen musulmi a yankin.

Pezeshkian ta ci gaba da cewa, alhakin da ke wuyan manyan kasashen musulmi ciki har da Saudiyya a halin da ake ciki a halin yanzu yana da nauyi, ya kuma kara da cewa: Idan kasashen musulmi suka hade kansu, to kuwa gwamnatin sahayoniyya ba za ta kuskura ta kai hari ko mamaye wata kasa ta musulmi ba, Saudiyya za ta iya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da hadin kan kasashen musulmi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan   September 16, 2025 Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida September 16, 2025 Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya September 16, 2025 An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna September 16, 2025 Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza September 16, 2025 Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A  HKI September 16, 2025 Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Ministan Tsaron Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi
  • Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara