Alakarmu da El-Rufai na nan babu matsala —Uba Sani
Published: 4th, February 2025 GMT
Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna, ya ce babu wata matsala tsakaninsa da tsohon uban gidansa kuma magabacinsa Malam Nasir El-Rufai.
Uba sani ya ce babu kamshin gaskiya a maganganun da ke yawa cewa shi da tsohon gwamnan El-Rufai suna zaman doya da manja.
Ya bayyana haka ne a yayin hirar da kafar tala bijin ta TVC ta yi da shi a ranar Litinin, inda ya ce “alakarmu tana nan yadda ta ke, babu wata matsala, kamar yadda ake rade-radi.
Am fara tunanin cewa dangantaka ta yi tsami tsakanin Uba da El-Rufai ne bayan da gwamnati mai cin ya yi zargin Gwamnatin El-Rufai da barin masa bashin biliyoyin Naira da kuma karkatar da wasu kudade.
Yau Majalisar za ta ci gaba da aiki kan Dokar Haraji Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Kano NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa BaA kwanakin baya Gwamnatin Uba Sani ta sallami wasu mukarraban El-Rufai da ke cikinta, masu rike da mukaman kwamishinoni kan zargin badakala.
Masu sharhi da magoya bayan tsohon gwamnan dai na zargin Gwamnatin Uba Sani da yi wa Nasir El-Rufai da mukarrabansa bi ta-da-kullin siyasa, zargin da ta karyata.
Zargin El-Rufai da karkatar da kudade, ya kai ga Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta kafa kwamitin binciken El-Rufai, wanda ta ce ta same shi da laifin da ake zargin sa, amma tuni ya musanta zargin.
Amma da aka yi wa gwamnan tambaya game da hakan, ya bayyana cewa bangaren majalisa na aiki ne a matsayin mai cin gashin kansa ba a karkashin gwamna ba, kuma suna da ’yancin gudanar da ayyukansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
Shugaban aksar Iran, Massoud Pezeshkian, ya bayyana cewa martanin sojojin kasarsa ga Isra’ila zai zama mafi muni idan hare-haren Isra’ilar suka ci gaba.
A wata tattaunawa ta wayar tarho da firaministan Pakistan Shehbaz Sharif, shugaban kasar Iran Massoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa dakarun gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran za su dauki kwararan matakan mayar da martani mai tsauri idan har gwamnatin Isra’ila ta ci gaba da kai farmaki kan Iran.
“Masu da’awar kare hakkin bil’adama ba wai kawai suna goyon bayan zaluncin gwamnatin sahyoniyawa ba ne, har ma suna karfafa mata gwiwar aikata wadannan munanan ayyuka ta hanyar ba ta makamai da kayan aiki,” in ji shi.
Mr. Pezeshkian ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila da ke samun goyon bayan Amurka da kasashen yammacin Turai ta sabawa dukkanin dokokin kasa da kasa.
A nasa bangaren, firaministan Pakistan ya bayyana goyon bayan kasarsa ga al’ummar iran, yana mai yin Allah wadai da keta hurumin kasar Iran da ‘yancinta, wanda ya zama cin zarafi ga dokokin kasa da kasa da kuma kundin tsarin mulkin MDD.
Sharif ya sake jaddada cewa Iran na da cikakken ‘yancin kare kanta a karkashin doka ta 51 na kundin tsarin mulkin MDD inda ya bayyana fatan ganin an dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.