Aminiya:
2025-06-15@19:00:58 GMT

EU ta yaba wa Gwamna Zulum kan farfaɗo da Jihar Borno

Published: 3rd, February 2025 GMT

Kungiyar Tarayyar Turai EU ta yaba wa ƙoƙarin Gwamna Babagana Umara Zulum wajen farfado da harkokin rayuwar al’ummar Jihar Borno bayan tashe-tashen hankulan ’yan ta’adda da jihar ta yi fama da shi.

EU ta buga misali da cibiyar koyar da sana’o’i ta Muna da ke horar da matasa musamman waɗanda rikicin Boko Haram ya shafa na tsawon fiye da shekaru goma.

Ya je Maiduguri daga Legas a kan keke Rikicin rusau ya yi ajalin mutum 4 a Kano

Shugaban tawagar Tarayyar Turai a Borno, Ambasada Gautier Mignot ne ya yi wannan yabon a Maiduguri a lokacin da yake zantawa da manema labarai a cibiyar koyar da sana’o’i ta Muna.

Ambasada Mignot ya ce tawagarsa ta yi matuƙar farin ciki da ganin irin damar da cibiyar sana’ar ta ke ba wa al’ummar jihar Borno da ma sauran su.

Ya ce, “Ina yabawa da wannan gagarumin nasara misali ɗaya ne na cibiyoyi da dama da gwamnatin jihar ta gina a ƙarƙashin jagorancin gwamna Zulum da hangen nesansa.

“Koyar da sana’o’i a bayyane yake – abu ne da matasa a jihar ke buƙata, kuma wannan wani abu ne da muka samu a Turai, musamman a Jamus.

“Mun yi nazari kan tarin ayyukan da taimakon jin kai da haɓaka haɗin gwiwa a fannoni da dama da Gwamnan ya aiwatar a Jihar Borno.

“Jihar Borno za ta kasance wani muhimmin yanki na haɗin gwiwar Turai a cikin shekaru masu zuwa.

Wakilin Jakadan Jamus, Karen Jensen, ya yaba wa Gwamna Zulum bisa yadda ya bai wa mata dama ta kowace fuska na rayuwa.

Jensen ya bayyana jin daɗinsa game da yawan mata da ke halartar shirye-shiryen koyar da sana’o’i daban-daban a cibiyar, musamman a fannonin da maza suka fi rinjaye kamar walda, tana mai cewa, “yana da muhimmanci mata su kasance sun samu ilimin sana’a.

“Ina alfahari da abin da nake gani a nan kuma aikin haɗin gwiwarmu yana da kyau sosai,” in ji Jensen.

Aminiya ta ruwaito cewa, tawagar ta je gidan gwamnati ne domin kai wa Gwamna Babagana Umara Zulum ziyara, inda Ƙungiyar Tarayyar Turai ta jaddada ƙudirinta na haɗa gwiwa da Gwamnatin Borno a ayyukan samar da zaman lafiya da hukumar haɗin kan kasa da kasa ta Jamus za ta aiwatar.

Da yake jawabi a wurin taron da ya gudana a Fadar Gwamnatin Borno, wakilin Hukumar Abinci da Aikin Noma na Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO) a Nijeriya da ECOWAS, Koffy Dominique Kouacou, ya yaba da salon jagorancin Gwamna Zulum wajen bunƙasa noma da ƙarfafa tattalin arzikin cikin gida ta hanyar kirkire-kirkire, samar da ababen more rayuwa da sauransu.

Ya ce za su yi aiki tare da Gwamnatin Zulum wajen gano hanyoyin da suka fi dacewa domin tallafa wa ƙoƙarin gwamnatin jihar ta hanyar inganta ayyukan noma, samar da tsarin abinci mai ɗorewa, da baiwa manoma da al’umma damar dogaro da kai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jihar Borno Gwamna Zulum jihar Borno Jihar Borno

এছাড়াও পড়ুন:

Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran

A yau Asabar aka gudanar da bikin ranar ” Idin Gadir” a nan birnin Tehran, wanda ya tashi daga dandalin “Inqilab” zuwa dandalin ” Azadi” mai nisan kilo mita 10. Bisa la’akari da halin yake da ake ciki, an bai wa bikin na bana taken: Iran ce, takobin Zulfikar Na Imam Ali.”

Miliyoyin mutane ne dai su ka cika filin bikin na birnin Tehran da mutane su ka fara taruwa tun da tsakar rana, har zuwa bayan faduwar rana. A bisa kirdado kusan  mutane miliyan 3 ne su ka taru a nan Tehran.

A cikin sauran birane da garuruwan Iran an yi wannan irin gangamin na raya ranar Idin Gadir wanda yake tattare da girmama shahidan da su ka kwanta dama sanadiyyar hare-haren ta’addancin HKI. Haka nan kuma mahalarta bikin na Gadir sun jinjinawa dakarun kare juyin musulunci na Iran da kuma sojojin kasar akan martanin da su ka mayarwa da HKI a daren jiya Juma’a da kuma a yau Asabar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya