EU ta yaba wa Gwamna Zulum kan farfaɗo da Jihar Borno
Published: 3rd, February 2025 GMT
Kungiyar Tarayyar Turai EU ta yaba wa ƙoƙarin Gwamna Babagana Umara Zulum wajen farfado da harkokin rayuwar al’ummar Jihar Borno bayan tashe-tashen hankulan ’yan ta’adda da jihar ta yi fama da shi.
EU ta buga misali da cibiyar koyar da sana’o’i ta Muna da ke horar da matasa musamman waɗanda rikicin Boko Haram ya shafa na tsawon fiye da shekaru goma.
Shugaban tawagar Tarayyar Turai a Borno, Ambasada Gautier Mignot ne ya yi wannan yabon a Maiduguri a lokacin da yake zantawa da manema labarai a cibiyar koyar da sana’o’i ta Muna.
Ambasada Mignot ya ce tawagarsa ta yi matuƙar farin ciki da ganin irin damar da cibiyar sana’ar ta ke ba wa al’ummar jihar Borno da ma sauran su.
Ya ce, “Ina yabawa da wannan gagarumin nasara misali ɗaya ne na cibiyoyi da dama da gwamnatin jihar ta gina a ƙarƙashin jagorancin gwamna Zulum da hangen nesansa.
“Koyar da sana’o’i a bayyane yake – abu ne da matasa a jihar ke buƙata, kuma wannan wani abu ne da muka samu a Turai, musamman a Jamus.
“Mun yi nazari kan tarin ayyukan da taimakon jin kai da haɓaka haɗin gwiwa a fannoni da dama da Gwamnan ya aiwatar a Jihar Borno.
“Jihar Borno za ta kasance wani muhimmin yanki na haɗin gwiwar Turai a cikin shekaru masu zuwa.
Wakilin Jakadan Jamus, Karen Jensen, ya yaba wa Gwamna Zulum bisa yadda ya bai wa mata dama ta kowace fuska na rayuwa.
Jensen ya bayyana jin daɗinsa game da yawan mata da ke halartar shirye-shiryen koyar da sana’o’i daban-daban a cibiyar, musamman a fannonin da maza suka fi rinjaye kamar walda, tana mai cewa, “yana da muhimmanci mata su kasance sun samu ilimin sana’a.
“Ina alfahari da abin da nake gani a nan kuma aikin haɗin gwiwarmu yana da kyau sosai,” in ji Jensen.
Aminiya ta ruwaito cewa, tawagar ta je gidan gwamnati ne domin kai wa Gwamna Babagana Umara Zulum ziyara, inda Ƙungiyar Tarayyar Turai ta jaddada ƙudirinta na haɗa gwiwa da Gwamnatin Borno a ayyukan samar da zaman lafiya da hukumar haɗin kan kasa da kasa ta Jamus za ta aiwatar.
Da yake jawabi a wurin taron da ya gudana a Fadar Gwamnatin Borno, wakilin Hukumar Abinci da Aikin Noma na Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO) a Nijeriya da ECOWAS, Koffy Dominique Kouacou, ya yaba da salon jagorancin Gwamna Zulum wajen bunƙasa noma da ƙarfafa tattalin arzikin cikin gida ta hanyar kirkire-kirkire, samar da ababen more rayuwa da sauransu.
Ya ce za su yi aiki tare da Gwamnatin Zulum wajen gano hanyoyin da suka fi dacewa domin tallafa wa ƙoƙarin gwamnatin jihar ta hanyar inganta ayyukan noma, samar da tsarin abinci mai ɗorewa, da baiwa manoma da al’umma damar dogaro da kai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jihar Borno Gwamna Zulum jihar Borno Jihar Borno
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa ya bukaci ma’aikatar kananan hukumomi da ta karfafa matakan yiwa kananan hukumomin jihar 27 jagoranci akan sha’anin mulki da harkokin kudi domin inganta ayyukan su.
Shugaban Kwamatin, Alhaji Aminu Zakari ya yi wannan kiran a karshen ziyarar kwanaki 3 da kwamatin ya yi a ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar a Dutse.
Alhaji Aminu Zakari wanda shi ne wakilin mazabar Gwiwa a majalisar dokokin jihar Jigawa, ya ce ziyarar kwamatin na da nufin tantance yadda ma’aikatar ta ke gudanar da ayyukan ta, ta fuskar harkokin mulki da na kudi da kuma dangantakar aiki tsakanin ta da kananan hukumomin jihar 27 kamar yadda tsarin mulki ya dorawa majalisa nauyi.
A nasa jawabin, mataimakin shugaban Kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama, Alhaji Sani Sale Zaburan ya bayyana bukatar ganin jami’an ma’aikatar da ke kula da kananan hukumomi a shiyya shiyya suna gudanar da ayyukan su ba tare da jingina da shugabannin kananan hukumomi ba a ko da yaushe amma Kuma su na yiwa kananan hukumomin jagoranci wajen gudanar da sha’anin mulki da harkokin Kudi kamar yadda ya kamata.
Daya daga cikin ‘yan kwamatin Malam Ibrahim Sabo Ahmad Roni ya duba kundin bayanan sha’anin mulki yayin da Oditoci su ka duba kundin bayanan harkokin Kudi tare da yabawa da kuma bada shawarwari da za su inganta ayyukan ma’aikatar.
Da ya ke mayar da jawabi, kwamishinan ma’aikatar kananan hukumomi Alhaji Ibrahim Garba Hannun Giwa wanda Babban Sakatare na maikatar ya wakilce shi, Alhaji Muhammad Yusha’u ya ce ma’aikatar ce ke uwa da makarbiya wajen yiwa kananan hukumomi jagoranci a sha’anin mulki da harkokin Kudi da zamantakewa domin kawo cigaba a yankunan karkara.
Kazalika, a daya bangaren kuma, karamin Kwamatin da Babban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar Dokokin jihar Jigawa ya kafa bisa jagorancin wakilin mazabar Kiyawa Alhaji Yahaya Muhammad Andaza domin duba aikin gyaran gidajen kananan hukumomin jihar 27 da ke kan titin Bypass a Dutse ya mika rahoton sa ga babban kwamatin.
Alhaji Yahaya Muhammad Andaza Wanda sakataren Kwamatin Alhaji Yusha’u Muhammad ya wakilta, ya ce karamin Kwamatin ya duba gidajen Inda ya dauki samfur din yanayin da su ke ciki.
Ya ce daga cikin gidajen akwai wadda ke funskatar matsaloli kamar na tsagewar bango da sanya darduma da kujeru da kayan amfani a dakin girki marasa inganci yayin da ba a mayar da na’urar sanyaya daki a wasu gidajen ba.
Yusha’u wanda shi ne mataimakin Akawun majalisar, ya lura cewa akwai rashin kyawun flasta a wasu gidajen yayin da kan dakin wasu ke yayyo sai Kuma rashin fankar sama da karayyayun kujeru da rashin hada wasu gidajen da wutar lantarki mai amfani da hasken rana da rashin kyawun kofofi da magudanin ruwa da ke kawo barazanar ambaliyar ruwa ga wasu gidajen.
A nasa jawabin, shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar Dokokin jihar Jigawa Alhaji Aminu Zakari ya ja hankalin shugabannin kananan hukumomin jihar da su dauki nauyin cikakkiyar kulawa ga gidajen bisa la’akari da dinbin kudaden da aka kashe wajen gyara gidajen.
Usman Mohammed Zaria