Da Ɗumi-ɗumi: Kotu Ta Dakatar Da Ohinoyi Na Masarautar Ebira
Published: 3rd, February 2025 GMT
Ko da yake har yanzu kotun ba ta bayar da cikakken bayani kan hukuncin ba, amma an gano cewa, shari’ar mai lamba HCO/05C/2024, Dakta Barnabas Adeku Ojiah da wasu mutane biyu ne suka shigar da ita, inda suke kalubalentar hukuncin tsohon gwamnan jihar na Kogi.
Sai dai, jin ta bakin Ohinoyi, Alhaji Ahmed Muhammed Tajani Anaje, ya ci tura yayin da wayoyin sa duk suke kashe a lokacin rubuta wannan rahoto.
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
Babban kwamandan dokarun khatamul Ambiya (s) a nan birnin Tehran ya bayyana cewa sojojinsa zasu ci gaba da fafatawa da HKI har zuwa lokacinda zata dakatar da kawowa Iran yaki, ko kuma ta sami nasara a kansu,
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Janar Ali Shudmoni, yana fadar haka a yau Lahadi bayan da suke cilla makamai masu linzami da kuma jiragen yaki wadanda ake sarrafasu da nesa kan HKI a karon farko na rana, a cikin kwanaki uku da fara yakin.
Janar Shodmani ya kara da cewa zasu ci gaba da kaiwa yahudawan hare-hare har zuwa lokacinda zasu yi nadama sun daina yakin.
Kwamnatin ya bayyana cewa ya zuwa yanzu sun saminar kasar lalata cibiyoyin da jiragen yakin HKI suke shan makamashi wanda yake basu damar isa kasar Iran don kai hare-hare. Banda haka akwai nasarori da dama da suka samu a hare-haren wadanda nan gaba zasu bayyana.