Aminiya:
2025-05-01@04:37:38 GMT

Arsenal ta yi sukuwar salla a kan Man City da ci 5

Published: 2nd, February 2025 GMT

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal ta yi sukuwar salla a kan Manchester City ta ci 5 da 1 a Gasar Firimiyar Ingila.

Ƙungiyoyin biyu sun ɓarje gumi da yammacin ranar Lahadi a filin wasa na Emirates, a mako na 24 na gasar.

Fasinjoji 30 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Ondo Asibitin Malam Aminu Kano ya hana motoci masu baƙin gilas shiga harabarsa

Ɗan wasan tsakiyar Arsenal, Martin Ordeegard ne ya fara jefa ƙwallo a minti na biyu da fara wasa.

Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Erling Haaland, ya warware ƙwallon da Arsenal ta jefa wa Manchester City, a minti na 55.

A minti ma 56 Thomas Partey ya ƙara jefa wa Arsenal ƙwallo ta biyu.

A minti ma 62 Lewis Skelly ya jefa ƙwallo ta uku, sai Kai Havertz ya jefa ƙwallo ta huɗu a minti na 76.

A minti na 93, ɗan wasan gaban Arsenal, Nwaneri ya ƙarƙare da ƙwallo ta biyar a raga.

Yanzu haka dai Liverpool ce ke jan ragamar teburin gasar da maki 56 daga wasanni 23, yayin da Arsenal ke biye mata da maki 50 daga wasanni 24.

Nottingham Forest tana mataki na uku, da maki 47 daga wasanni 24 s teburin gasar.

Ita kuwa Manchester City na mataki na huɗu a teburin gasar da maki 41 daga wasanni 24 da ta buga.

Manchester City na ci gaba da fuskantar matsaloli tun bayan da wasu manyan ’yan wasanta suka samu rauni, kuma a baya-bayan nan kyaftin ɗinta Kyle Walker ya bar ƙungiyar zuwa AC Milan da ke ƙasar Italiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arsenal Firimiya Ordeegard daga wasanni

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki

Kazalika, domin daidaita ci gaban cinikayyar waje, manufofin da za a aiwatar sun hada da na tallafawa kamfanonin dake fitar da hajoji, ta yadda za su rage hadurra daka iya aukuwa, da fadada fitar da hidimomin da ake samarwa ga karin sassan duniya, da karfafa gwiwar kamfanonin waje, ta yadda za su kara zuba jarinsu a kasar ta Sin.

 

Daga nan sai jami’in ya bayyana cewa, Sin na da isassun manufofi da tsare-tsare, da za su wanzar da burinta na raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma a shekarar nan ta bana. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • Yadda ta kaya a wasannin kusa da na ƙarshe na Gasar Zakarun Turai
  • DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • HOTUNA: Yadda aka dawo da ’yan Najeriya 203 daga Libya
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115