Aminiya:
2025-11-02@21:12:50 GMT

Harkar tsaro a gabashin Sakkwato na ƙara taɓarɓarewa — Sanata Lamiɗo

Published: 12th, September 2025 GMT

Sanata Ibrahim Lamiɗo, mai wakiltar Sakkwato ta Gabas, ya nuna damuwarsa kan yadda matsalar tsaro ke ƙara tsananta a yankinsa, inda ya ce hare-hare da satar mutane sun zama ruwan dare.

A hirarsa da manema labarai, Sanatan ya ce: “Gaskiya abin tsoro ne rayuwa a Gabashin Sakkwato. Kusan kowace rana sai an kai hari, an kashe mutane ko kuma an sace su.

Muna cikin tashin hankali sosai.”

’Yan bindiga sun harbi fasinjoji 2, sun sace makiyaya a Neja Gwamna ya aike wa majalisa dokar haramta auren jinsi ɗaya a Kano

Ya bayyana cewa duk da ƙoƙarin da yake yi wajen ganin an kawo gyara, wasu ’yan siyasa suna kawo cikas.

Sai dai ya ce ba zai fasa jajircewa wajen ganin an ƙara yawan jami’an tsaro da sansanonin da ke Ƙananan Hukumomin Raɓah da Sabon Birni.

Sanata Lamiɗo ya yi addu’ar Allah Ya bai wa jama’ar yankin haƙuri, tare da roƙon Ubangiji ya hukunta waɗanda suke da hannu a ta’addancin.

Ya kuma yi suka ga ’yan siyasar da suke jira sai an yi mummunan lamari sannan su je jaje, maimakon su tsaya tsayin daka a magance matsalar tsaro da su.

A cewarsa, “Idan aka inganta tsaro, mutane za su iya yin noma da sana’o’insu, wannam shi ne taimakon da ya fi muhimmanci.”

Yankin Gabashin Sakkwato na daga cikin wuraren da suka fi fama da hare-hare da satar mutane, lamarin da ya kawo wa harkar noma, kasuwanci da makarantu cikas.

Mutanen yankin sun buƙaci gwamnati ta haɗa kai da sauran shugabanni domin nemo mafita game da matsalar tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hare hare Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific

Babban Kwamishinan Kare Hakkin Dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya soki hare-haren sama da Amurka ta kai wa jiragen ruwa a yankin Caribbean da Pacific, wanda ya kasance keta dokokin kare hakkin dan adam na duniya.

“An ruwaito cewa an kashe mutane sama da 60 a jerin hare-haren da sojojin Amurka ke kai wa jiragen ruwa a Caribbean da Pacific tun farkon watan Satumba, wadanda ake zargin suna da hannu a safarar miyagun kwayoyi, a cikin wani yanayi da ba su da hujja a karkashin dokokin kasa da kasa,” in ji Volker Turk a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Juma’a.

Babban jami’in Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana hare-haren a matsayin “abin da ba za a yarda da shi ba” kuma ya bukaci Washington da ta “kawo karshen irin wadannan hare-hare ta kuma dauki dukkan matakan da suka dace don hana kisan gillar da ake yi wa mutanen da ke cikin wadannan jiragen ruwa ba bisa ka’ida ba, ba tare da la’akari da laifukan da ake zarginsu da aikatawa ba.”

Amurka ta yi ikirarin cewa wadannan ayyuka wani bangare ne na yaki da safarar miyagun kwayoyi da ta’addanci.

Duk da haka, Turk ya nuna cewa yaki da safarar miyagun kwayoyi a kan iyakoki “al’amari ne na tilasta bin doka.”

“Dangane da ƙarancin bayanai da hukumomin Amurka suka bayyana a bainar jama’a, da alama mutanen da ke cikin jiragen ruwan da aka kai hari ba su da wata barazana ga rayukan wasu, kuma ba a yi amfani da karfin soji mai tsanani a kansu ba a karƙashin dokokin kasa da kasa,” in ji shi.

Volker Turk ya yi kira da a “yi bincike mai zaman kansa cikin sauri, kuma ya yi kira ga Amurka da ta yaki fataucin na haramtacciyar hanya ta hanyar kamawa, da gurfanar da wadanda ake tuhuma cikin adalci, da kuma bin ka’ida.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure