Aminiya:
2025-09-18@00:44:36 GMT

Mamakon ruwan sama ya hallaka mutum 3 a Zariya

Published: 10th, September 2025 GMT

Wani mamakon ruwan sama da aka tafka a birnin Zariyan jihar Kaduna, ya yi sanadiyar mutuwar mutum uku yayin da kuma ake ci gaba da neman gawar mutum daya.

Bayanai sun nuna cewa biyu daga cikin wadanda suka rasa ransu dalibai ne, Fatima Sani Danmarke mai shekara 18, da ke karatu a makarantar share fagen shiga jami’a da ke Funtua a jihar Katsina da Yusuf Surajo da shi kuma yake karatu a Zariya, sai kuma yarinyar da Fatima ke goye da ita.

DSS ta warware tankiyar da ke tsakanin NUPENG da Dangote ’Yan bindiga sanye da hijabi sun sace mutane 11 a Zamfara

Wani da lamarin ya faru a gabansa, Mallam Mustapha Badamasi Danbakano, ya ce, “Bayan ruwa ya ɗan yi sauƙi sai muka hangi wani mai babur mai kafa uku yana kokarin sauke wata yarinya goye da wata karamar yarinya a bayanta.

“To sakamakon ruwan saman da ya rufe ko ina ba a iya gane a inda kwalbati yake, ita kuma tana ja da baya don neman inda za ta tsallaka kawai sai ta faɗa cikin kwalbatin ita da goyon da take dauke da shi.

“Shima kuma mai babur din sai ya shiga ciki domin ya ceto su, nan take ruwan ya wuce da su gaba daya,” in ji shi.

Ya kara cewa daga nan ne sai wani dalibi mai suna Yusuf Surajo da ke gefe ya zaburo da gudu ya fada ruwan da nufin ya ceto su, shi ma haka ruwan ya tafi da shi.

Imam Mallam Musa Umar Almishawi Wanda ya jagoranci sallar jana’izar dalibin ya ce marigayin ya sami babban rauni a goshinshi sakamakon bugun da wani karfe da ya yi masa a cikin ruwan.

Ita kuwa daliba Fatima da goyon ta na ’yar shekara uku ba a riga anyi jana’izar su ba zuwa lokacin da ake hada wannan rahoton.

Aminiya ta gano cewar ya zuwa yanzu an gano gawarwakin mutane uku a daidai gadar makarantar firamare ta Isan Nabawa da ke unguwar Tudun Wada Zariya.

Sai dai har yanzu ana ci gaba da kokarin gano gawar matukin babur mai kafa ukun amma ba a kai ga gano shi ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliya ruwan sama Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu

Hukumar Tsaron Farin Kaya a Nijeriya DSS, ta gurfanar da fitaccen ɗan gwagwarmayar nan, Omoyele Sowore a kotu.

A ƙunshin ƙarar da DSS ta gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta haɗa da shafukan sada zumunta na X da kuma Facebook, inda take zarginsu da ba da ƙofar aibata Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku

Darekan shigar da ƙara na Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya, M.B Abubakar da wasu lauyoyi huɗu —M.E. Ernest da U.B. Bulla da C.S. Eze da kuma E.G. Orubor, ne suka shigar da ƙarar a madadin Gwamnatin Tarayya da kuma hukumar ta DSS.

DSS wadda ta kafa hujja da sashe na 24 da ke cikin kundin dokokin yanar gizo, ta ce Sowore ya yi amfani da shafukansa na dandalan sada zumunta na X da Facebook wajen wallafa wani saƙo da ke cin mutuncin Shugaba Tinubu.

Tun dai a farkon watan nan ne DSS ta buƙaci goge wani saƙo da ɗan gwagwarmayar ya wallafa wanda ta riƙa a matsayin bayanan ƙarya, cin zarafi ta yanar gizo da kalaman haddasa ƙiyayya, waɗanda kuma ta ce na iya haddasa rikici su kuma ɓata sunan Najeriya a ƙasashen waje.

Sai dai har zuwa ranar Litinin, 15 ga watan Satumba, babu wani mataki da aka ɗauka na goge saƙon da DSS ɗin ta buƙata.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta