Aminiya:
2025-11-02@19:36:13 GMT

’Yan bindiga sun kashe jami’an NSCDC 8, sun sace ɗan China a Edo

Published: 6th, September 2025 GMT

Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kai hari yankin Okpella, da ke Ƙaramar Hukumar Etsako ta Gabas, a Jihar Edo, inda suka kashe wasu jami’an tsaro.

Sun kashe jami’an Sibil Difens guda takwas sannan suka yi garkuwa da wani ma’aikacin ƙasar China.

APC ta yi barazanar hukunta “Yaran Badaru” a Jigawa Yadda makarantu ke tatsar kuɗaɗe daga iyayen ɗalibai

Haka kuma, sun jikkata wasu jami’an Sibil Difens h6udu da wani mutum, waɗanda yanzu haka suna asibiti inda ake kula da ita.

Jami’an da lamarin ta shafa suna tsaron ma’aikatan ƙasar China na Kamfanin Simitin BUA.

Suna kan hanyarsu na zuwa wajen da suke aikin siminti lokacin da aka tare su a bakin kofar shiga kamfanin.

’Yan bindigar, ɗauke da makamai suka buɗe musu wuta inda suka kashe jami’ai takwas nan take.

Sun sace ɗaya aga cikin ma’aikatan ƙasar China, sauran huɗun an ceto su cikin ƙoshin lafiya.

Wani babban jami’in NSCDC ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya faru da misalin ƙarfe 10 na dare.

Yanzu haka hukumomin tsaro sun fara aikin haɗin gwiwa don bincike a dajin da ke kusa yanki , domin kuɓutar da wanda aka sace.

Kwamandan NSCDC na Jihar Edo, Gbenga Agun, ya ziyarci wajen da lamarin ya faru da kuma jami’an da suka jikkata a asibiti.

Mai magana da yawun hukumar a jihar, Efosa Ogbebor, ya ce ofishin hedikwatar hukumar ne kawai zai fitar da sanarwa a hukumance.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

“Amurka ba za ta tsaya kawai tana kallo ba yayin da irin waɗannan ta’addancin ke faruwa a Nijeriya da sauran ƙasashe.

“Mun shirya, muna da ƙarfi da niyyar kare Kiristoci a faɗin duniya,” in ji Trump.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano October 31, 2025 Manyan Labarai Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m