Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Published: 5th, September 2025 GMT
Yakin ya farkar da Sin da duniya baki daya, wanda ya zama tushen kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, daga bisani kuma ya dora kasar bisa tafarkin zamani. Ga duniya, mulkin mallaka ya fara wargajewa. Kasashe da dama sannu a hankali suka fahimci cewa, in sun jajirce, za su samu ‘yancin kai.
Tasirin yaki da zalunci da danniya da Jama’ar Sinawa suka yi, ya sa kasar ta kudiri aniyar yaki da zalunci da danniya a duniya ta rungumi manufar tabbatar da zaman lafiya, inda ta nuna wa duniya cewa, lokacin wariya da danniya, tsarin rayuwar dabbobi (na sama ya buge na kasa), ba zai dore ba amma samar da dawwamammen zaman lafiya da tsaro, na sama ya yi wa na kasa adalci, shi ne tsarin da ya dace kowa ya runguma.
Wannan fareti na nunawa duniya cewa, sojojin jama’ar kasar Sin an tanade su ne don tabbatar da zaman lafiya da aminci, inda yake a rubuce jikin alluna da tutoci, “Adalci zai yi nasara,” “samar da zaman lafiya zai yi nasara,” da kuma “mutane za su yi nasara”.
Daga cikin kasashe biyar na dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya (MDD), kasar Sin ta ba da gudummawar mafi yawan dakarun kiyaye zaman lafiya a fadin duniya.
A ’yan kwanakin nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping a lokacin wani taron tattauna bukatun tsarin shugabancin duniya, ya yi nuni da cewa, kasar Sin za ta yi aiki kafada-da-kafada da kasashen duniya domin samar da “tsarin shugabanci na duniya mai adalci da daidaito”.
Wannan ya tabbatar da cewa, yakin da jama’ar Sinawa suka yi a kan yakin zalunci da danniya daga Japanawa bai tsaya nan kadai ba har ma da neman wa sauran kasashe masu tasowa ’yancin zaman lafiya da ci gaba mai dorewa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: zaman lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
An gudanar da taron tattaunawa na duniya kan kirkire-kirkire da bude kofa da ci gaba na bai daya, jiya Juma’a a birnin Lagos na Nijeriya. Yayin taron wanda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG da karamin ofishin jakadancin Sin dake Lagos suka shirya, ministan kula da harkokin matasa na Nijeriya Ayodele Olawande da shugaban CMG Shen Haixiong, sun gabatar da jawabai ta kafar bidiyo.
A cewar ministan na Nijeriya, cikin shekaru 5 da suka gabata, dubban matasan kasar sun ci gajiyar tallafin karatu da shirye-shiryen horo da na musaya da Sin ta samar, kuma wannan hadin gwiwa da ake yi a aikace ya kara fahimta da aminci tsakanin kasashen biyu. Ya kara da cewa, a shirye ma’aikatarsa take ta karfafa hadin gwiwa da sassa masu ruwa da tsaki na kasar Sin wajen ci gaba da fadada shirye-shiryen musaya da na hadin gwiwa da suka shafi matasa.
A nasa bangare, Shen Haixiong ya ce a matsayinta na babbar kafar yada labarai dake watsa shirye shiryenta ga sassa daban daban na duniya, tashar talabijin ta CCTV dake karkashin CMG da abokan huldarta, za su yayata shawarar Sin ta jagorantar harkokin duniya da gabatar da tafarkin Sin na zamanantar da kanta da karfinta na kirkire kirkire a sabon zamani ga al’ummar duniya. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA