Hisbah ta kama masu safarar mutane da mata 12
Published: 4th, September 2025 GMT
Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama wani da ake zargi da safarar mutane (wanda aka sakaya sunansa) a wani wurin garejin motoci tare da wasu mata 12 da ake zargi da safarar mutane da ke shirin tafiya Legas.
Bayanin hakan ya fito ne daga bakin mataimakin Kwamandan Hukumar ta Hisbah, Sheikh Mujahideen Aminuddeen.
Sanarwar ta bayyana cewa, jami’an rundunar sun kama mutumin ne a wani garejin motoci da ke kan titin Zariya.
Hukumar ta bakin mataimakin ta bayyana cewa, jami’an Hisbah ƙarƙashin jagorancin OC Muhammad Bashir na garejin motoci sun kama wakilin safarar wanda aka ce ya fito daga Jihar Borno, ya hau mota zuwa Legas tare da waɗanda ake zargin.
Aminuddeen ya bayyana cewa, bayanan farko sun nuna cewa, mutumin yana safarar matan ne, kowannensu yana da fasfo na ƙasa da ƙasa zuwa ƙasar Saliyo ta hanyar Legas, Jamhuriyar Benin da Ghana, inda ya ƙara da cewa mutumin yana da shirin yin biza ga waɗanda ya yi safarar don tafiya ƙasar Saudiyya don neman aiki.
Aminuddeen ya kuma bayyana cewa, a yayin da ake yi musu tambayoyi, matan sun sanar da jami’an Hisbah cewa kowaccen su ta biya Naira miliyan 1,500,000 a karon farko tare da yarjejeniyar biyan cikon sauran kuɗi idan sun samu aiki a inda za su.
A cewar hukumar, ɗaya daga cikin matan akwai mai shekara 50 sauran biyu kuma akwai mai shekara 23 da mai shekara 20, yayin da ragowar kuma ’yan shekara 15 ne.
Ya bayyana cewa a cikin waɗanda aka yi safarar, uku sun fito daga Katsina, biyu daga Kano, ɗaya daga jihohin Borno, Jigawa da Zamfara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar Hisbah Jigawa bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
Sojojin Najeriya sun kashe aƙalla mayakan ƙungiyar ISWAP 8, ciki har da manyan kwamandojinta biyu a Jihar Borno.
Wata majiyar leƙen asiri daga rundunar haɗin kai ta OPHK ta bayyana cewa an kashe ’yan ta’addan ne a wata arangama da suka yi da sojojin a kan hanyar Maiduguri zuwa Baga a safiyar ranar Litinin.
DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabalaA cewar majiyoyin, an yi arangamar ce a kusa da Garin Giwa da ke gab da ƙauyen Kauwa, lokacin da ’yan ta’addan suka yi wa dakarun da ke sintiri kwanton ɓauna.
“A yayin wannan artabu, an kashe ’yan ta’adda takwas, ciki har da Munzirs biyu (kwamandojin filin daga na ƙungiyar) da kuma Qaid ɗaya (shugaban sashe).
“An kashe Modu Dogo, Munzir daga Dogon Chukun, wani Munzir da ba a bayyana ba, da Abu Aisha, shugaban sashe (Qaid) daga Tumbun Mota,” in ji wata majiya.
Majiyar ta ƙara da cewa wasu mayaƙa da dama sun samu raunuka, musamman waɗanda suka tsere da ƙafa bayan sun yi watsi da babura 14 da sojojin suka ƙwato.