Kungiyar Masana’antu Ta Yi Fatali Da Sake Gabatar Da Haraji Na Kaso 4 Na Kwastom
Published: 29th, August 2025 GMT
Ajayi-Kadri ya ce kungiyar ta yi cikakken nazari kan sake gabatar da harajin na FOB wanda ta tabbatar zai kara dagula lamura ne kawai da sake jefa masana’antu cikin mawuyacin hali.
“Gaskiyar lamarin ita ce, farashin kashi hudu cikin 100 na kamfanonin ya yi yawa fiye da yadda aka samu karin kashi bakwai cikin dari da kuma karin kashi daya cikin dari na harajin tsarin shigo da kayayyaki,” in ji shi.
Ya kara da cewa, a sauran kasashen yammacin Afirka kamar Ghana, Cote d’Iboire, da Senegal, ana tsare-tsaren da aka yi niyya ko tattara kudade a tsakanin kashi 0.5 zuwa kashi daya cikin 100 na FOB, tare da karin haraji kawai kan kayan alatu ko kuma wadanda ba su da muhimmanci a shigo da su.
“Hukuncin da hukumar kwastam ta Nijeriya ta yi na bai daya na kakaba harajin kashi hudu cikin 100 na FOB zai kara tsadar kasuwanci, da karfafa hanyoyin da ba a saba gani ba, zai haifar da karkatar da kaya da kuma kara tsanani,” in ji shugaban.
Ajayi-Kadri ya nemi gwamnatin tarayya da hukumar Kwastam da su janye matakin kakaba harajin kaso hudu na FOB domin kyautata tattalin arziki ko kuma a jinkita aiwatar da hakan har sai nan gaba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi
“A lokacin, mun yi lissafin adadi a Babban Bankin. Na tashi na kafa sharuda bisa ga ka’idodi, inda na ce a cire tallafin yau. Farashin kaya zai tashi daga kashi 11 zuwa kashi 13, zan rage shi a cikin shekara guda. Ba za mu samu hauhawar farashin kaya na kusan kashi 30 ba,” in ji shi.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA