Ambaliya: Manoma sun yi asarar miliyoyin Naira a Taraba
Published: 28th, August 2025 GMT
Sanadiyyar ambaliyar ruwa a gonaki amfanin gona na miliyoyin Naira ne suka salwanta inda ɗaruruwan filayen noma suka shefe da ruwa a Jihar Taraba.
Kodayake, ba a bayyana ko an sako ruwa daga Logdo Dam ba ne daga jamhuriyar Kamaru ba, amma kogin Benuwe da ke Taraba ya yi ta malala daga gaɓarsa wanda ya yi sanadin ambaliya da lalata ɗaruruwan filayen noma.
Daily Trust ta gano cewa ruwan ya fara ƙaruwa a kogi a ’yan kwanakin da suka gabata, kuma a yanzu kogin ya yi ta malala a gefan koguna inda ya haddasa ambaliya a faɗin jihar.
Ambaliyar ta shafi wasu yankunan sassan Ƙananan hukumomin Lau da Karim_Lamido da Gassol da Ardo-kola
Gonakin da ambaliyar ta shafa sun haɗa da: Da na Shinkafa da Masara galibi da ke kusa da kogin Benuwe sun lalace yayin da gidaje da dama a ƙauyukan da ke gefen kogin Benuwe kuma suka nutse.
Alhaji Sale Binnari, a Ƙaramar hukumar Karim-Lamido ya shaida wa Daily Trust cewa ruwa ya lalata ɗaruruwan gonakin shinkafa da masara.
Garba Halilu, a garin Mutum-Biyu, Ƙaramar hukumar Gassol ya kuma shaida wa Daily Trust cewa, ambaliyar ruwa ta lalata gonaki da dama a yankunan Mutum Biyu da yankin Kwatan Nanido da Maigemu da Sheka.
Ya ce, kogin ya malala a rassan gaɓarsa, sakamakon haka ɗaruruwan filayen noma ne suka nutse da ruwa.
Hakimin kauyen Sheka a Ƙaramar hukumar Gassol, Alhaji Haruna Sheka ya kuma ce gonaki da dama sun nutse da ruwa sakamakon ambaliya da ruwan kogin Benuwe.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliya Lau da Karim Lamido da Gassol da Ardo kola Taraba
এছাড়াও পড়ুন:
NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya (NDLEA) ta kama wani ɗan ƙasar Indiya tare da wasu mutane uku bisa zargin shigo da ƙwayoyin Tramadol da aka ƙiyasta darajarsu ta kai naira biliyan uku (N3bn) zuwa cikin ƙasar.
A cewar NDLEA, wannan shi ne kamen ƙwayoyi mafi girma da hukumar ta yi a cikin shekarar nan, lamarin da ke nuna yadda safarar miyagun ƙwayoyi ke ƙaruwa a ƙasar.
Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a NijarCikin wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta bayyana cewa jami’anta sun kama mutanen ne a filin jirgin sama na Murtala Muhammad da ke Legas, bayan sun samu bayanan sirri da suka taimaka wajen gano su.
NDLEA ta bayyana cewa ƙwayoyin Tramadol ɗin da aka gano an shigo da su ne cikin kwalaye a matsayin maganin multivitamins, yayin da ake ƙoƙarin fitar da su daga filin jirgin a wasu manyan motoci.
“Ƙwayoyin da aka kama ba su da wata alaƙa da amfani na lafiya, waɗanda aka shigo da su a ɓoye a matsayin maganin rage kasala da ƙara kuzari (multivitamins),” in ji sanarwar NDLEA.
Rahotanni sun nuna cewa a da likitoci na bayar da Tramadol ne don rage zafi da raɗaɗin ciwo, amma yanzu ta zamo annoba musamman a tsakanin matasa, wadda ke haddasa mummunan maye da illa ga lafiya.
Hukumar ta nuna damuwa game da yadda yawan masu amfani da Tramadol ke ƙaruwa ba wai a Najeriya kaɗai ba, har ma a wasu ƙasashen Afirka, duk da illolin da ƙwayar ke haddasawa, kamar matsalolin taɓin hankali ko ma rasa rai gaba ɗaya.