Rikici Yana Ci Gaba Da Gudanar A Kasar Sudan Tsakanin Sojoji Da Dakarun Kai Daukin Gaggawa
Published: 3rd, June 2025 GMT
Rikici tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na kasar yana ci gaba da habaka a wurare da dama na kasar
Kasar Sudan dai na fuskantar tabarbarewar harkokin tsaro cikin hanzari, a daidai lokacin da ake ci gaba da gwabza fada tsakanin sojoji da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces (RSF), a cikin sarkakkiyar yanayin jin kai da na siyasa da kuma fadadan rikici a jihohi daban-daban.
Fadace-fadace a Sudan suna ci gaba da karuwa, inda ake ci gaba da gwabza fada tsakanin sojoji da mayakan kungiyar Rapid Support Forces, inda sojojin saman Sudan suka zafafa kai hare-hare ta sama ta hanyar amfani da jiragen sama marasa matuka ciki, kuma suka yi luguden wuta kan wasu muhimman wurare na kungiyar Rapid Support Forces a jihar Kordofan ta Arewa.
Hare-haren sun fi tsanani ne a yankin Kilo Zero dake arewacin Bara da Ummu Sayala, tare da lalata motocin soji da kayayyakin aiki, baya ga hasarar dimbin dakarun kungiyar Rapid Support Forces, kamar yadda majiyoyi da dama suka tabbatar da nasarar sojojin Sudan kan ‘yan tawaye.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Rapid Support Forces
এছাড়াও পড়ুন:
Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano
Mazauna unguwar Zangon Kaya da ke karamar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano sun shiga cikin makoki sakamakon nutsewar da wasu matasa hudu suka yi a hanyar ruwa da baraguzan gine-gine suka tushe.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Yusif, ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin.
A cewarsa, lamarin ya faru ne bayan wadanda lamarin ya rutsa da su suka shiga mashigar ruwa da suka taru sakamakon toshewar hanyar jirgin da ake yi.
Ya kara da cewa, kamar yadda shaidun gani da ido suka bayyana, da farko biyu daga cikin wadanda abin ya shafa sun shiga cikin ruwan da nufin yin iyo amma sun makale. A kokarin ceto su, mutum na uku ya shiga, shi ma ya makale. Abin baƙin ciki, mutum na huɗu, yana ƙoƙari ya ceci sauran, ya fuskanci irin wannan matsalar.
Saminu ya yi nuni da cewa, kafin isowar hukumar kashe gobara mazauna yankin sun yi nasarar ceto biyu daga cikin wadanda abin ya shafa. Yayinda “Sauran biyun, tawagar ceto ta fito da
Wadanda abin ya shafa sun hada da Nasirudden Tasi’u dan shekara 25 da Basir Sani mai shekaru 28 da Yakubu Muhd dan shekara 22 da Usman Ubale dan shekara 26.
Jami’in hulda da jama’a ya yi nuni da cewa, an samu dukkanin mutane hudun a sume kuma daga baya aka tabbatar da sun mutu.
“An mika gawar su ga SP Abdulkadir M. Albasu na sashin ‘yan sanda na Dawanau domin ci gaba da bincike”.
Saminu ya ce, Daraktan hukumar kashe gobara ta jiha Alhaji Sani Anas ya jajantawa iyalan mamatan.
Ya kuma gargadi jama’a da su guji shiga cikin ruwa ba tare da izini ba ko kuma masu hadari, musamman wadanda ayyukan gine-gine ya shafa.
“Muna kira ga ‘yan ƙasa da su guji yin iyo ko wasa a cikin kududdufi, musamman waɗanda aka toshe ko ba a tsara su don amfani da nishaɗi ba.
Al’umma na ci gaba da nuna alhininsu yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike kan al’amuran da suka dabaibaye wannan mummunan lamari.
Rel/Khadijah Aliyu