Bishop Joseph Osifuwa, Bishop na jihar Kwara, ya ce Nijeriya za ta iya magance matsalar rashin tsaro da ake fama da ita a sassan kasar nan idan har ta dauki matakin magance masu tada kayar baya.

 

Bishop Osifuwa ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a gefen babban taron cocin karo na 35 a Ilorin.

 

A cewarsa, magance rashin tsaro bai kamata ya zama matsala ga kasar da ta hada karfi da karfe a ayyukan wanzar da zaman lafiya na kasa da kasa domin murkushe ‘yan tawaye ba.

 

Ya kuma shawarci gwamnati da kada ta rinka yi masu tada kayar baya ta hanyar yi musu afuwa, ya kara da cewa kada gwamnati ta tausayawa ‘yan tada kayar baya da ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

 

Bishop Osifuwa ya bukaci gwamnati da ta rufe idanunta ta magance su, inda ya ce su mutane ne ba basu da imani.

 

Ya zargi gwamnonin jihohi da tabarbarewar tattalin arzikin ‘yan kasa, yana mai cewa gwamnonin na rashin adalci ga jama’arsu.

 

Malamin ya ce gwamnonin na karbar makudan kudade a kowane wata daga Gwamnatin Tarayya ba tare da wani tasiri da ya yi daidai da rayuwar mutane ba.

 

Bishop Osifuwa, ya yabawa shugaban kasa Bola Tinubu kan sakin kudi ga gwamnonin jihohi.

 

Ya yi kira ga shugabannin siyasa da na addini da su inganta hadin kai, yana mai gargadin cewa kabilanci ko addini na iya kawo barazana ga zaman lafiya da ci gaba.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — Amnesty

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta Amnesty International, ta ce Gwamnatin Tarayya ta yi sakaci game da ɓacewar ɗan gwagwarmaya Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata.

A wata sanarwa da ta fitar, Amnesty, ta ce abin takaici ne ganin cewa shekara shida kenan da Dadiyata ya ɓace ba tare da wani sahihin bayani ba.

Mutum ɗaya ya rasu, an jikkata wasu yayin arangama da ’yan sanda a Abuja Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a Neja

Dadiyata ya ɓace ne a ranar 2 ga watan Agustan 2019, bayan wasu mutane ɗauke da makamai sun shiga gidansa da ke unguwar Barnawa a Jihar Kaduna, suka tafi da shi.

Tun daga wannan lokacin, iyalansa da abokansa ke jiran jin wani abu game da ɓacewarsa, amma har yanzu babu bayani.

Shugaban Amnesty a Najeriya, Isa Sanusi, ya ce Dadiyata mutum ne mai kishin ƙasa kuma yana da kishi wajen faɗin gaskiya a kafafen sada zumunta.

Ya ce akwai yiwuwar ɓacewar Dadiyata na da alaƙa da irin sukar da yake yi wa gwamnati da wasu ‘yan siyasa.

Ko da yake gwamnati ta musanta cewa tana da hannu, Amnesty ta ce dole gwamnati ta ɗauki alhakin binciken abin da ya faru da bayyana gaskiya domin rage wa iyalan Dadiyata raɗaɗi.

Ƙungiyar ta kuma buƙaci hukumomin tsaro su yi bincike mai zurfi, su kuma bayyana sakamakon da suka samu.

Ta ce abin takaici ne a ce shekara shida kenan ba tare da wani bayani dangane da ɓacewarsa ba.

Hakazalika, Amnesty ta buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu, da ya sa baki cikin lamarin domin a san halin da ake ciki.

Ta ce lokaci na ƙurewa, iyalan Dadiyata suna buƙatar amsa guda ɗaya kan inda ya shiga.

Wanda suka halarci taron manema labaran sun haɗa da matarsa Khadija Lame da ƙaninsa Usman Idris.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — Amnesty
  • Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
  • ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
  • Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba
  • GORON JUMA’A 01-07-2025
  • Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
  • NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi?
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu