Bishop Joseph Osifuwa, Bishop na jihar Kwara, ya ce Nijeriya za ta iya magance matsalar rashin tsaro da ake fama da ita a sassan kasar nan idan har ta dauki matakin magance masu tada kayar baya.

 

Bishop Osifuwa ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a gefen babban taron cocin karo na 35 a Ilorin.

 

A cewarsa, magance rashin tsaro bai kamata ya zama matsala ga kasar da ta hada karfi da karfe a ayyukan wanzar da zaman lafiya na kasa da kasa domin murkushe ‘yan tawaye ba.

 

Ya kuma shawarci gwamnati da kada ta rinka yi masu tada kayar baya ta hanyar yi musu afuwa, ya kara da cewa kada gwamnati ta tausayawa ‘yan tada kayar baya da ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

 

Bishop Osifuwa ya bukaci gwamnati da ta rufe idanunta ta magance su, inda ya ce su mutane ne ba basu da imani.

 

Ya zargi gwamnonin jihohi da tabarbarewar tattalin arzikin ‘yan kasa, yana mai cewa gwamnonin na rashin adalci ga jama’arsu.

 

Malamin ya ce gwamnonin na karbar makudan kudade a kowane wata daga Gwamnatin Tarayya ba tare da wani tasiri da ya yi daidai da rayuwar mutane ba.

 

Bishop Osifuwa, ya yabawa shugaban kasa Bola Tinubu kan sakin kudi ga gwamnonin jihohi.

 

Ya yi kira ga shugabannin siyasa da na addini da su inganta hadin kai, yana mai gargadin cewa kabilanci ko addini na iya kawo barazana ga zaman lafiya da ci gaba.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar? November 2, 2025 Wasanni Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025? November 1, 2025 Wasanni Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara