Bishop Joseph Osifuwa, Bishop na jihar Kwara, ya ce Nijeriya za ta iya magance matsalar rashin tsaro da ake fama da ita a sassan kasar nan idan har ta dauki matakin magance masu tada kayar baya.

 

Bishop Osifuwa ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a gefen babban taron cocin karo na 35 a Ilorin.

 

A cewarsa, magance rashin tsaro bai kamata ya zama matsala ga kasar da ta hada karfi da karfe a ayyukan wanzar da zaman lafiya na kasa da kasa domin murkushe ‘yan tawaye ba.

 

Ya kuma shawarci gwamnati da kada ta rinka yi masu tada kayar baya ta hanyar yi musu afuwa, ya kara da cewa kada gwamnati ta tausayawa ‘yan tada kayar baya da ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

 

Bishop Osifuwa ya bukaci gwamnati da ta rufe idanunta ta magance su, inda ya ce su mutane ne ba basu da imani.

 

Ya zargi gwamnonin jihohi da tabarbarewar tattalin arzikin ‘yan kasa, yana mai cewa gwamnonin na rashin adalci ga jama’arsu.

 

Malamin ya ce gwamnonin na karbar makudan kudade a kowane wata daga Gwamnatin Tarayya ba tare da wani tasiri da ya yi daidai da rayuwar mutane ba.

 

Bishop Osifuwa, ya yabawa shugaban kasa Bola Tinubu kan sakin kudi ga gwamnonin jihohi.

 

Ya yi kira ga shugabannin siyasa da na addini da su inganta hadin kai, yana mai gargadin cewa kabilanci ko addini na iya kawo barazana ga zaman lafiya da ci gaba.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatan Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna za su tsunduma yajin aiki
  • Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
  • Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
  • Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda
  • Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan
  • Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku
  • FCCPC Ta Sammaci Air Peace Kan Rashin Maido Da Kuɗin Tikitin Jirgin Da Aka Soke Tafiyarsa
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Durƙushewar Sababbin Sana’o’i Tun Ba A Je Ko’ina Ba
  • An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai