Gobara ta lalata shagunan kasuwar waya a Kwara
Published: 1st, May 2025 GMT
Wata gobara da ta tashi a yammacin ranar Laraba a wata shahararriyar kasuwar wayoyin salula da ke ‘Challenge Market’, a Ilorin babban birnin Jihar Kwara, ta yi mummunar ɓarna.
Gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 9:06 na dare kuma ana kyautata zaton wutar lantarki ce ta haddasa ta.
Dalilin da ya sa aka samu fashewar abubuwa a barikin Maiduguri – Sojoji ’Yan fashin teku sun sace mata 4 a hanyar ruwa ta BayelsaKasuwar tana da shaguna sama da 120, rumfunan 80, da wasu wuraren kasuwancin wayar da yawa.
A wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta Jihar Kwara, Hassan Adekunle ya fitar a ranar Alhamis, ya ce gobarar ta fi shafar shagunan waya da wuraren gyara.
“Nan take jami’an kashe gobararmu suka taru suka isa wurin inda suka tarar da shaguna da dama sun ƙone da wuta,” in ji shi.
“Kasuwar ta ƙunshi shaguna sama da 120, rumfuna 80 da sauran wuraren kasuwanci masu yawa. Ta hanyar shiga tsakani cikin gaggawa, da ƙwararrun dabaru, jami’an sun yi nasarar daƙile yaɗuwar gobarar, tare da taƙaita tasirinta zuwa rumfuna 10 kawai.
“Wuraren da gobarar ya shafa dai sun haɗa da shagunan waya da kuma wuraren gyaran waya, binciken farko ya nuna cewa wutar lantarki ce ta tashi.
“ ’Yan kasuwa da masu ruwa da tsaki a kasuwar sun yabawa hukumar kashe gobara ta Jihar Kwara bisa saurin ɗaukar matakin da suka yi wajen ceto kasuwar daga gobarar da ta ɓarke.”
Daraktan hukumar kashe gobara ta jihar Falade Olumuyiwa ya jajantawa shugabannin kasuwar da ’yan kasuwar da gobarar ta shafa.
Olumuyiwa ya kuma yi addu’ar Allah Ya dawo masu da dukkan asarar da aka samu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kwara kashe gobara
এছাড়াও পড়ুন:
Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Ondo ta tabbatar da kama wata mata mai suna Iluyemi Bosede bisa zargin kashe yayarta, Tewogboye Omowumi, a Akure, babban birnin jihar.
A cewar sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Olayinka Ayanlade, ya fitar a ranar Talata, ya ce lamarin ya faru ne a ranar shida ga Satumba, 2025, bayan wata sa’insa da ta kaure tsakanin matar da marigayiyar kan Naira 800.
Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin NajeriyaJami’in ya bayyana cewa Bosede ta ture ’yar uwarta har ta faɗi ƙasa, lamarin da ya haifar da mutuwarta.
Ya ce, “Binciken farko ya nuna cewa Iluyemi Bosede ta je wurin yayar tata, Tewogboye Omowumi mai shekaru 35, domin karbar bashinta na N800 na kudin tumatir da barkono. Sai dai tankiyar da ta fara a matsayin ƙaramin sabani ta rikide zuwa tashin hankali, inda ake zargin Bosede ta riƙe kayan marigayiyar har ta faɗi ƙasa.”
“Abin takaici, duk da an garzaya da marigayiyar asibiti don samun kulawar gaggawa, likitoci sun tabbatar da mutuwarta tun kafin a fara ba ta taimako. Wannan lamari ya nuna yadda ƙaramin sabani zai iya rikidewa zuwa mummunar husuma idan ba a magance shi cikin lumana ba.”
Bayan faruwar lamarin, rundunar ta ce ta kama wadda ake zargi kuma tana tsare da ita a halin yanzu, yayin da bincike ke ci gaba.
Rundunar ta kuma tabbatar da cewa za a gurfanar da wadda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike, domin ta girbi abin da ta shuka.