Aminiya:
2025-05-01@20:24:13 GMT

Gobara ta lalata shagunan kasuwar waya a Kwara

Published: 1st, May 2025 GMT

Wata gobara da ta tashi a yammacin ranar Laraba a wata shahararriyar kasuwar wayoyin salula da ke ‘Challenge Market’, a Ilorin babban birnin Jihar Kwara, ta yi mummunar ɓarna.

Gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 9:06 na dare kuma ana kyautata zaton wutar lantarki ce ta haddasa ta.

Dalilin da ya sa aka samu fashewar abubuwa a barikin Maiduguri – Sojoji ’Yan fashin teku sun sace mata 4 a hanyar ruwa ta Bayelsa

Kasuwar tana da shaguna sama da 120, rumfunan 80, da wasu wuraren kasuwancin wayar da yawa.

Rahotanni sun ce gobarar ta shafi rumfuna 10.

A wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta Jihar Kwara, Hassan Adekunle ya fitar a ranar Alhamis, ya ce gobarar ta fi shafar shagunan waya da wuraren gyara.

“Nan take jami’an kashe gobararmu suka taru suka isa wurin inda suka tarar da shaguna da dama sun ƙone da wuta,” in ji shi.

“Kasuwar ta ƙunshi shaguna sama da 120,  rumfuna 80 da sauran wuraren kasuwanci masu yawa. Ta hanyar shiga tsakani cikin gaggawa, da ƙwararrun dabaru, jami’an sun yi nasarar daƙile yaɗuwar gobarar, tare da taƙaita tasirinta zuwa rumfuna 10 kawai.

“Wuraren da gobarar ya shafa dai sun haɗa da shagunan waya da kuma wuraren gyaran waya, binciken farko ya nuna cewa wutar lantarki ce ta tashi.

“ ’Yan kasuwa da masu ruwa da tsaki a kasuwar sun yabawa hukumar kashe gobara ta Jihar Kwara bisa saurin ɗaukar matakin da suka yi wajen ceto kasuwar daga gobarar da ta ɓarke.”

Daraktan hukumar kashe gobara ta jihar Falade Olumuyiwa ya jajantawa shugabannin kasuwar da ’yan kasuwar da gobarar ta shafa.

Olumuyiwa ya kuma yi addu’ar Allah Ya dawo masu da dukkan asarar da aka samu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwara kashe gobara

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok

Mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun kashe masu zaman makoki bakwai tare da jikkata wasu a ƙauyen Kopl da ke Ƙaramar Hukumar Chibok ta Jihar Borno.

Shugaban Karamar Hukumar, Honorabul Modu Mustapha, ya ce mayaƙan sun buɗe wa mutanen wuta ne a yammacin ranar Litinin, a yayin da suke shirin gudanar da addu’o’i ga ’yan uwansu da suka rasu.

Ya ce, “Sun taru ne domin yin addu’a lokacin da ’yan ta’addan suka sauka a kansu. Mun kwashe mutane da yawa da suka samu raunukan harsashi zuwa Babban Asibitin Mubi da ke maƙwabtaka da Jihar Adamawa.

“Adadin waɗanda suka mutu na iya ƙaruwa, saboda wasu sun tsere cikin daji da raunukan harsashi. Ana ci gaba da aikin nemowa da ceto waɗanda ke cikin daji,” in ji shi.

Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu

Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya ci gaba da yin Allah wadai da hare-haren, inda ya bayyana halin da ake ciki a matsayin abin da ya wuce tunanin dan Adam.

“Ko jiya ma, na samu kiran gaggawa cewa an kashe sama da ’yan banga 10 a wani yankin da ke tsakanin Karamar Hukumar Hawul ta Jihar Borno da garin Garkida a Jihar Adamawa.

“Al’ummata na fama da munanan asara ba tare da wani faɗa ba. A cikin wata guda da ya gabata kaɗai, an kashe sama da mutum dari a hare-hare da dama yankunan Sabon Gari da Izge da Kirawa da Pulka da Damboada Chibok da Askira Uba da wasu da yawa da ba zan iya lissafawa ba,” in ji Sanata Ndume.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin Boko Haram Da ISWAP: An Kashe Masunta 18, Mutane  Da Yawa Sun Bace
  • Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno