Shi dai filin jirgin saman, wanda gwamnatin Umaru Bago ta gina a Jihar Neja, an raɗa masa sunan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

 

Jirgin kasuwancin na farko mallakin kamfanin Overland Air mai lamba 5N-CCN ya sauka ne da misalin ƙarfe 1:32 na rana.

 

Cikin fasinjojin akwai Gwamnan Jihar Neja, Umaru Bago, Minista Mohammed Idris, tsohon Gwamnan Neja Dakta Babangida Aliyu, Ƙaramin Ministan Harkokin Noma da Samar da Abinci, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi, da wasu manyan jami’an gwamnati.

 

Ministan ya yaba wa Shugaba Tinubu saboda samar da yanayin da ya bai wa filin jirgin damar fara aiki, yana mai cewa hakan na nuna jajircewar Shugaban Ƙasa wajen inganta ababen more rayuwa a faɗin ƙasar.

 

Haka kuma, Ministan ya jinjina wa Gwamna Bago bisa hangen nesa da jajircewar sa na buɗe Jihar Neja ga cigaban noma da kasuwanci da masana’antu da kuma inganta tattalin arzikin jihar.

 

Ya ce: “Dole ne mu yaba wa shugaban ƙasar mu kamar yadda gwamnan mu ya faɗa. Wannan haƙiƙa mafarki ne da ya zama gaskiya. Gwamnan ne ya sa hakan ya tabbata. Yana da kwaɗayin ganin Jihar Neja ta buɗe ƙofar cigaba ta fannin noma, kasuwanci, masana’antu da kuma bunƙasar tattalin arziki.”

 

A nasa jawabin, Gwamna Bago ya ce wannan jirgi na farko wani ɓangare ne na buɗe jihar zuwa ga duniya baki ɗaya.

 

Ya ce: “Shugabannin kamfanin Overland sun nuna karamci matuƙa wajen ba mu wannan sabon jirgi daga Legas zuwa Minna, sannan yanzu daga Minna zuwa Abuja, kuma hakan zai riƙa faruwa sau uku a mako – a ranakun Litinin, Laraba da Juma’a. Wannan jirgi ne na buɗe hanya – buɗe Jihar Neja ga sararin samaniyar duniya.

 

“Muna son gode wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, wanda filin jirgin ya samu suna daga gare shi, saboda ya ba mu dukkan goyon bayan da muke buƙata.”

 

Gwamna Bago ya ƙara da cewa jihar tana da niyyar amfani da filin jirgin wajen fitar da kayan amfanin gona zuwa ƙasashen waje don haɓaka tattalin arzikin jihar da zama ɗaya daga cikin manyan masu fitar da kayan noma daga Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

  Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki

Majiyar tsaron kasar ta Kamaru sanar da cewa, da dama daga cikin sojojin kasar sun rasa rayukansu sanadiyyar wani hari da kungiyar Bokoharam ta kai musu ta hanyar amfani da manyan bindigogi da kuma jirgin sama maras matuki akan iyaka da Najeriya.

Majiyar ta ce an kai harin ne a yankin Sagami dake kusa da tafkin Chadi a gundumar Logun mai iyaka da kasar Najeriya.

Ita dai kungiyar Bokoharam ta addabi kasashen Najeriya, Kamaru da kuma jamhuriyar Nijar. Yankun arewacin kasar ta Kamaru ya fara fuskantar kai hare-hare daga wannan kungiyar ne tun a 2014 wanda kuma har yanzu yana ci gaba da faruwa daga lokaci zuwa lokaci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje
  •   Iran  Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35  Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  • Babu wanda ya tsira daga hatsarin Jirgin Air India mai dauke da fasinjoji 242
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki