New York Times : Amurka na son rage ofisoshin jakadncinta a Afirka
Published: 21st, April 2025 GMT
Wani rahoto da jaridar New York Times ta Amurka ta fitar ya nuna cewa Amurka na neman rage kasantuwarta a duk duniya musamman a Afirka.
Jaridar ta bayyana wani daftarin dokar shugaban kasa na sirri wanda ya tanadi “sake tsara tsarin ma’aikatar harkokin wajen Amurka.
Sai dai ministan harkokin wajen kasar Marco Rubio, ya musanta wadannan shirye-shiryen.
Batu na farko na shirin sake fasalin ma’aikatar harkokin wajen Amurka shi ne rage ofisoshin ma’aikatar harkokin wajen Amurka a bangaren sauyin yanayi, dimokuradiyya, da kare hakkin bil’adama, batutuwan da gwamnatin Trump ta shiga kafar wando guda dasu.
Rahoton ya ce rage kasafin kudin zai kai ga rufe ofisoshin jakadanci a kasashen waje, amma inda Amurka za ta rage yawan aikin diflomasiyya shi ne a Afirka.
Domin Washington ta yi imanin cewa akwai yankuna hudu kawai a duniya inda kasancewarta zai kasance mai mahimmanci: Eurasia, Gabas ta Tsakiya, Latin Amurka da Asiya-Pacific.
Don haka Afirka Amurka za ta samar da jakada na musamman kan harkokin Afirka.” wanda zai kai rahoto ga Majalisar Tsaro ta Fadar White House, ba Ma’aikatar Harkokin Wajen ba.
Kudirin ya kuma bayyana cewa “za a rufe dukkan ofisoshin jakadanci da karamin ofishin jakadancin da ba su da mahimmanci a yankin Saharar Afirka.” A ƙarshe, duk sauran ayyukan da suka rage za a hada su karkashin ikon manzo na musamman.
An shirya aiwatar da wadannan sauye-sauye a ranar 1 ga Oktoba, a cewar jaridar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: aikatar harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata
Gwamnatin Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba wa wasu daidaikun mutane da kamfanoni na kasar.
Cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar, ta ce irin wannan mataki da bangare guda ya dauka ba zai taimaka wajen cimma abubuwan da ake buri ba, ciki har da cimma zaman lafiya a Sudan, da kare tsaro da zaman lafiyar duniya.
Sanarwar ta ce, gwamnatin Sudan na bayyana cewa, hanya mafi dacewa ta warware rikici ita ce tattaunawa kai tsaye, maimakon dogaro da zato, wanda wasu masu manufa ta siyasa suka kitsa, wadanda ba su dace da muradun al’ummar Sudan ba.
Sanarwa ta nanata cewa, samun zaman lafiya a kasar, babban batu ne da al’ummarta a ko ina ke buri.
Ta kara da tabbatar da cewa, hakkin gwamnatin Sudan ne cika burin tabbatuwar zaman lafiya ta kowacce hanya, ciki har da tattaunawa da hada hannu da dukkan bangarori.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 An Zabi Issa Tchiroma A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A Kamaru September 14, 2025 Kasar Iran Ta Yi Fatali Da Zarge-Zargen Da Kungiyar G7 Da Kawayenta Suka Yi Kanta September 14, 2025 Iran Ta Bayyana Shirinta Na Halartar Taron Shekara-Shekara Na Hukumar Makamashin Nukiliya September 14, 2025 Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bayyana Rashin Halarta Tawagarta A Kada Kuri’a Kan Batun Falasdinu September 14, 2025 Tsananin Masifar Da Falasdinawa Ke Ciki A Gaza Saboda Hare-Haren Gwamnatin Mamayar Isra’ila September 14, 2025 Amurka Ta Ce; Harin Isra’ila Kan Birnin Doha Ba Zai Shafi Kawancenta Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Ba September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci