New York Times : Amurka na son rage ofisoshin jakadncinta a Afirka
Published: 21st, April 2025 GMT
Wani rahoto da jaridar New York Times ta Amurka ta fitar ya nuna cewa Amurka na neman rage kasantuwarta a duk duniya musamman a Afirka.
Jaridar ta bayyana wani daftarin dokar shugaban kasa na sirri wanda ya tanadi “sake tsara tsarin ma’aikatar harkokin wajen Amurka.
Sai dai ministan harkokin wajen kasar Marco Rubio, ya musanta wadannan shirye-shiryen.
Batu na farko na shirin sake fasalin ma’aikatar harkokin wajen Amurka shi ne rage ofisoshin ma’aikatar harkokin wajen Amurka a bangaren sauyin yanayi, dimokuradiyya, da kare hakkin bil’adama, batutuwan da gwamnatin Trump ta shiga kafar wando guda dasu.
Rahoton ya ce rage kasafin kudin zai kai ga rufe ofisoshin jakadanci a kasashen waje, amma inda Amurka za ta rage yawan aikin diflomasiyya shi ne a Afirka.
Domin Washington ta yi imanin cewa akwai yankuna hudu kawai a duniya inda kasancewarta zai kasance mai mahimmanci: Eurasia, Gabas ta Tsakiya, Latin Amurka da Asiya-Pacific.
Don haka Afirka Amurka za ta samar da jakada na musamman kan harkokin Afirka.” wanda zai kai rahoto ga Majalisar Tsaro ta Fadar White House, ba Ma’aikatar Harkokin Wajen ba.
Kudirin ya kuma bayyana cewa “za a rufe dukkan ofisoshin jakadanci da karamin ofishin jakadancin da ba su da mahimmanci a yankin Saharar Afirka.” A ƙarshe, duk sauran ayyukan da suka rage za a hada su karkashin ikon manzo na musamman.
An shirya aiwatar da wadannan sauye-sauye a ranar 1 ga Oktoba, a cewar jaridar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: aikatar harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
Ya ce Jihar Kurus Ribas ita ce ta farko a yankin kudu da ta shiga a dama da ita a harkar noman alkama, lamarin da ke nuni da gayar nasara wajen samar da abinci a kowani sassa na kasar nan.
Kyari ya kara da cewa shirin rabar da takin zamani ya taimaka wajen bunkasa samar da shinkafa zuwa tan 58,000, lamarin da ya bai wa gwamnatin tarayya sanya tallafi a bangaren rabar da shinkafa ga jihohin da ambaliyar ruwa ta shafa.
Ministan ya ce akwai bukatar kare masu amfani da kuma kayan da ake nomawa, “kaso 80 cikin 100 na abincinmu manoman cikin gida ne suka samar da su.”
A daidai gabar da ake hasashen adadin ‘yan Nijeriya zai kai miliyan 400 a nan da shekarar 2050, Kyari ya ce gwamnati ta dukufa wajen kyautata harkar noma da kuma samar wa matasa ayyukan yi a matsayin mataki mai dogon zango na samar da wadatar abincin.
Ya ce gwamnati na kuma kokarin gyara kadarorin da kasar ke da su kamar su taraktoci, da sauran muhimman kayan aiki domin kara bunkasa samar da abinci.
Ya kuma ce Nijeriya ta yi hadin gwiwa da kasar Belarus don samar da ayyukan hadaka da nufin kara yawan kayan da ake fitarwa.
Ministan ya yi gargadin cewa a guji amfani da injinan noma da gwamnati ta samar ba ta hanyoyin da suka dace ba, inda ya bukaci manoma da su yi amfani da irin wadannan kayan aikin yadda ya kamata.
Ministan ya ce warare uku na ajiyar kaya wato silo ne kawai suke aiki a halin yanzu, inda ya sha alwashin cewa za a maida hankali wajen gyara sauran.
Kyari ya ce “Ma’aikatar noma da dawata kasa da abinci za ta hada kai da masu ruwa da tsaki don tabbatar da an yi amfani da wadannan muhimman wuraren ajiyar kaya.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp