Sakatare-janar na kungiyar Hizbullah Sheikh Naim Qassem ya yi Allah wadai da kalaman da kiraye kirayen da ake na “kwance damarar” kungiyar Hizbullah, yana mai kiransa da cewa wani yunkuri ne na raunata kasar Lebanon da kuma ci gaba da fadada manufofin Tel Aviv.

Sheikh Naim Qassem ya bayyya hakan ne a wani jawani da ya gabatar da kai tsaye ta talabijin jiya Juma’a.

Kalaman nasa na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma a karshen shekarar da ta gabata da nufin kawo karshen kazamin rikicin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane kusan 4,000 a kasar Labanon.

Sheikh Qassem ya jaddada cewa ci gaba da kokarin da gwamnatin Isra’ila ke yi na kawo cikas ga diyaucin kasar Labanon da tsayin daka zai fuskanci martani marar iyaka.

Ya kuma jaddada cewa, karfi da hadin kan kungiyar Hizbullah da sojojin kasa da al’ummar kasar Labanon ya tabbatar da cewa gwamnatin ba za ta cimma manufofinta ba.

Sheikh Qassem ya kuma gargadi gwamnatin Isra’ila, inda ya bayyana cewa kungiyar gwagwarmayar Lebanon na da zabi da dama a gabanta dangane da keta hurumin da Tel Aviv ta yi na tsagaita bude wuta da kungiyar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita

JMI ta bayyana cewa zata yi amafani da hakkinta wanda doka ya bata na ficewa daga yarjeniyar NPT don sake farfado da takunkuman tattalin arziki na MDD a kan kasar.

Jakadan kasar Iran a MDD, Amir Saeid Iravani ne ya bayyana haka a jiya Laraba.

Kamfanin dillanbcin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Iravani yana fadar haka a wata wasika da ya rubutawa kwamitin tsaro na MDD a jiya. Ya kuma kara da cewa Iran zata yi amfani da dokokin da suka bada damar yin hakan.

Kasashen Turai guda Uku jamusa Farana da Burtania suna son su yi amfani da damar da ake kira snap back don sake farfado da takunkuman MDD a kan kasar na yarjeniyar JCPOA.

Ya kammala da cewa yarjeniyar JCPOA bata da amfanmi bayan da suka kauracewa yin aiki da ita na shekaru.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita
  • Ministan Tsaro Na Kasar Iran ya bada Labarin Gwajin Wani Sabom Makami Mai Limzami Mai Daukar abubuwan Fashewa Har Ton Biyu
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar