Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya ce hare-haren da sojojin Amurka ke kaiwa kasar Yemen da keta hurumin yankunanta barazana ce karara ga zaman lafiya da tsaron kasa da kasa.

A cikin wata sanarwa da ya fitar yau Juma’a, Baghaei ya yi tir da hare-haren da Amurka ke kai wa Yemen ba bisa ka’ida ba, wanda ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula da raunata jama’ar kasar tare da lalata kayayyakin more rayuwa na kasar.

Ya ce ya kamata kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kawo karshen rashin daukar mataki da kuma yin shiru dangane da farmakin da sojojin Amurka ke kaiwa Yemen.

Ya ce Amurka na ci gaba da kai hare-haren soji kan kasar Yemen tare da kai hari kan kayayyakin more rayuwa na kasar domin daukar fansa kan hadin kan al’ummar Yemen da goyon bayan al’ummar Palastinu da ake zalunta.

Kakakin na Iran ya ce hare-haren na Amurka cin zarafi ne ga ka’idojin Yarjejeniya Ta Majalisar Dinkin Duniya da kuma ka’idojin dokokin kasa da kasa.

Baghaei ya dorawa gwamnatin Amurka alhakin aikata laifuka.

Kafofin yada labaran kasar Yemen sun ruwaito a safiyar yau Juma’a cewa, an kai wasu sabbin hare-hare a babban birnin kasar Yemen, inda aka kai hari kan wani sansanin soji a kudancin Sana’a da wasu hare-hare guda hudu.

An kuma kai hare-hare a yankunan da ke kusa da filin jirgin sama na Sana’a, baya ga gundumomi biyu a kudanci da tsakiyar lardin Sana’a.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) sun kaddamar da wani sabon harin makamai masu linzami da jirage marasa matuka kan Isra’ila a cikin daren jiya Asabar, biyo bayan matakin farko na harin ramuwar gayya na kan harin Isra’ila na ranar Juma’a.

Jim kadan bayan harba makamai masu linzami da jirage marasa matuka, sashen hulda da jama’a na IRGC ya ba da sanarwar kaddamar da wani sabon shiri na manyan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka.

Sanarwar ta yi nuni da cewa, sashen kula da sararin samaniya na IRGC ya fara wannan sabon mataki na aikin a matsayin mayar da martani kai tsaye ga sabbin ta’addancin gwamnatin sahyoniyawan.

Babban abin da aka fi mayar da hankali kan wannan sabon farmakin na ‘Operation True Promise III’ an bayar da rahoton cewa, birnin Haifa mai tashar jiragen ruwa ya kunshi muhimman wuraren soji da masana’antu na gwamnatin.

Hare-haren sun shafi wasu muhimman cibiyoyin soji da masana’antu na Isra’ila, da suka hada da matatun mai da na wutar lantarki a Haifa, inda aka ce gobara ta tashi a sanadiyar haka.

Daya daga cikin faifan bidiyon ya nuna wata gagarumar gobara da ta tashi a matatar mai ta Haifa bisa tasirin da manyan makamai masu linzami na Iran suka yi, wanda ya haskaka sararin samaniyar yankunan da aka mamaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya