Barcelona za ta yi asarar maki saboda saɓa dokar FIFA a wasanta da Osasuna
Published: 28th, March 2025 GMT
Akwai yiwuwar Barcelona za ta yi asarar maki saboda saɓa wata dokar Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA) a wasan gasar La Liga wanda ta doke Osasuna.
Rahotanni na cewa ƙungiyar Osasuna za ta shigar da ƙorafi kan wasan da Barcelona ta doke ta da ci 3-0, saboda zargin saɓa dokar FIFA kan amfani da ɗan wasan da bai cancanta ba.
A jiya Alhamis ce Barcelona ta karɓi baƙuncin Osasuna a wani kwantan wasa na gasar La Liga, inda to doke baƙin nata da ci 3-0.
Wannan nasarar ta bai wa Barcelona damar yin zaman faɗi da tazarar maki 3 a saman teburin La Liga da jimillar maki 63, bayan buga wasanni 28.
Sai dai wasan ya bar baya da ƙura, saboda Osasuna na zargin Barcelona ta karya wata dokar FIFA kan amfani da wani ɗan wasa yayin karawar.
Osasuna na zargin cewa ɗan wasan baya na Barcelona, Inigo Martinez wanda ɗan asalin Sifaniya ne, bai cancanci buga wasan ba.
A kakar bana, tauraruwar Martinez na haskawa tun bayan zuwan sabon koci Hansi Flick ƙungiyar, wanda ya sa ɗan wasan ya samu kiranye daga tawagar ƙasarsa Sifaniya a watan nan.
Sai dai ɗan wasan ya samu rauni a gwiwa, lamarin da ya tilasta masa baro tawagar Sifaniya da ke buga gasar UEFA Nations League, inda aka maye gurbinsa da ɗan wasan Bournemouth, Dean Huijsen.
Sai dai kuma bayan ya baro tawagar ta Sifaniya, Martinez ya dawo ƙungiyarsa ta Barcelona, inda ya buga wasan da suka yi nasara kan Osasuna a ranar Alhamis.
Shafin Goal ya ambato wata jaridar wasanni ta Sifaniya, Diario Sport, na cewa Osasuna na duba yiwuwar shigar da ƙorafi kan Barcelona saboda zargin taka dokar FIFA dangane da saka ɗan wasan da ya baro tawagar ƙasarsa.
Osasuna na ganin cewa, bai kamata a ce Martinez ya buga wasan ba saboda dokar FIFA ta ce ‘yan wasan da suka baro tawagar ƙasarsu ba za su buga wa ƙungiyarsu wasa ba har sai bayan aƙalla kwanaki biyar, face idan hukumar ƙwallo ta amince masa ya buga
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barcelona
এছাড়াও পড়ুন:
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
Dan wasan da ya lashe kyautar a bara, Ademola Lookman na Nijeriya ba ya cikin jerin ‘yan wasan da aka lissafo a bana, inda hukumar kwallon kafa ta Afirka (Caf) ta samar da kwamitin kwararru wanda ya zakulo masu horarwa da ‘yan wasan da suka “Taka rawar gani” a tsakanin 6 ga watan Janairu zuwa 15 ga watan Oktoban wannan shekara.
An bayyana sunan mai horar da tawagar ‘yan kwallon kafa ta kasar Cape Berde, Bubista a matsayin mai neman lashe kyautar mai horarwa mafi kwazo bayan jagorantar tawagar kasar ta Blue Sharks wajen samnun gurbin gasar kofin duniya a karon farko a tarihi.
Haka nan tawagar ta tsibirin Cape Berde na cikin masu gogayyar lashe kungiya mafi hazaka a shekarar, tare da Morocco wadda a baya-bayan nan ta lashe kofin duniya na gasar kwallon kafa ta ‘yan kasa da shekara 20.
‘Yanwasa mata na Nijeriya Esther Okoronkwo da Rasheedat Ajibade na cikin wadanda ke neman lashe kyautar zakarun ‘yanwasa mata na Afirka na wannan shekarar. Ya zuwa yanzu dai hukumar CAF ba ta bayyana ranar da za a yi bikin bayar da kyautar ba.
Dan wasa mafi Kwazo: Andre-Frank Zambo Anguissa (Napoli da Kamaru), Denis Bouanga (Los Angeles FC da Gabon), Serhou Guirassy (Borussia Dortmund da Guinea), Achraf Hakimi (Paris St-Germain da Moroko), Oussama Lamlioui (Renaissance Berkane), Fiston Mayele (Pyramids da DR Congo), Iliman Ndiaye (Eberton da Senegal), Bictor Osimhen (Galatasaray da
Nigeria), Mohamed Salah (Liberpool da Masar), Pape Matar Sarr (Tottenham Hotspur da Senegal).
Mai tsaron raga na maza: Yassine Bounou (Al Hilal da Moroko), Aymen Dahmen (CS Sfadien da Tunisia), Marc Diouf (TP Mazembe da Senegal), Edouard Mendy (Al-Ahli da Senegal), Munir Mohamedi (RS Berkane da Moroko), Stanley Nwabali (Chippa Utd da Nijeriya), Andre Onana
(Trabzonspor da Kamaru), Ahmed El Shenawy (Pyramids da Masar), Bozinha (Chabes da Cape Berde), Ronwen Williams (Mamelodi Sundowns da Afirka ta Kudu).
Mai horar da kungiyar maza: Bubista (Cape Berde), Moine Chaabani (Renaissance Berkane), Hossam Hassan (Masar), Krunoslab Jurcic (Pyramids), Mohamed Ouahbi (Moroko U20), Romuald Rakotondrabe (Madagascar), Walid Regragui (Moroko), Tarik Sektioui (Moroko U23), Pape Thiaw (Senegal), Sami Trabelsi (Tunisia).
Tawagar maza: Algeria, Cape Berde, Masar, Ghana, Ibory Coast, Moroko, Moroko U20, Senegal, Afirka ta Kudu, Tunisia. ‘Yan wasa Mata da ke takarar lashe zakarun Afirka na shekara ta 2025.
‘Yar wasa mafi kwazo: Rasheedat Ajibade (Paris St-Germain da Nijeriya), Barbra Banda (Orlando Pride da Zambia), Portia Boakye (Hapoel Petah Tikba da Ghana), Tabitha Chawinga (Lyon da Malawi), Temwa Chawinga (Kansas City da Malawi), Ghizlaine Chebbak (Al Hilal da Moroko), Mama Diop (Strasbourg da Senegal), Rachael Kundananji (Bay FC da Zambia),
Sanaa Mssoudy (AS FAR da Moroko), Esther Okoronkwo (AFC Toronto da
Nijeriya).
Mai tsaron raga na mace: Sedilame Boseja (Mamelodi Sundowns da Botswana), Andile Dlamini (Mamelodi Sundowns da Afirka ta Kudu), Habiba Emad (FC Masar da Masar), Khadija Er-Rmichi (AS FAR da Moroko), Fatoumata Karantao (MUSFAS Bamako da Mali), Cynthia Konlan (Swieki United da Ghana), Adji Ndiaye (AS Bambey da Senegal), Fideline Ndoy (TP
Mazembe da DR Congo), Chloe N’Gazi (Marseille da Algeria), Chiamaka Nnadozie (Brighton & Hobe Albion da Nijeriya).
Mai horar da kungiyar mata: Genobeba Anonman (15 de Agosto), Kim Bjorkegren (Ghana), Lamia Boumehdi (TP Mazembe), Desiree Ellis (Afirka ta Kudu), Carol Kanyemba (Zambia U17), Adelaide Koudougnon (Ibory Coast U17), Justin Madugu (Nijeriya), Bankole Olowookere (Nijeriya U17), Siaka Gigi Traore (ASEC Mimosas), Jorge Bilda (Moroko).
Tawagar mata: Kamaru U17, Ghana, Ibory Coast U17, Mali, Morocco, Nijeriya, Nijeriya U17, Afirka ta Kudu, Tanzania, Zambia U17. Za ku iya ganin cikakken jerin wadanda ke neman lashe kyautukan a shafin hukuma Caf. [1]
ShareTweetSendShare MASU ALAKA