Barcelona za ta yi asarar maki saboda saɓa dokar FIFA a wasanta da Osasuna
Published: 28th, March 2025 GMT
Akwai yiwuwar Barcelona za ta yi asarar maki saboda saɓa wata dokar Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA) a wasan gasar La Liga wanda ta doke Osasuna.
Rahotanni na cewa ƙungiyar Osasuna za ta shigar da ƙorafi kan wasan da Barcelona ta doke ta da ci 3-0, saboda zargin saɓa dokar FIFA kan amfani da ɗan wasan da bai cancanta ba.
A jiya Alhamis ce Barcelona ta karɓi baƙuncin Osasuna a wani kwantan wasa na gasar La Liga, inda to doke baƙin nata da ci 3-0.
Wannan nasarar ta bai wa Barcelona damar yin zaman faɗi da tazarar maki 3 a saman teburin La Liga da jimillar maki 63, bayan buga wasanni 28.
Sai dai wasan ya bar baya da ƙura, saboda Osasuna na zargin Barcelona ta karya wata dokar FIFA kan amfani da wani ɗan wasa yayin karawar.
Osasuna na zargin cewa ɗan wasan baya na Barcelona, Inigo Martinez wanda ɗan asalin Sifaniya ne, bai cancanci buga wasan ba.
A kakar bana, tauraruwar Martinez na haskawa tun bayan zuwan sabon koci Hansi Flick ƙungiyar, wanda ya sa ɗan wasan ya samu kiranye daga tawagar ƙasarsa Sifaniya a watan nan.
Sai dai ɗan wasan ya samu rauni a gwiwa, lamarin da ya tilasta masa baro tawagar Sifaniya da ke buga gasar UEFA Nations League, inda aka maye gurbinsa da ɗan wasan Bournemouth, Dean Huijsen.
Sai dai kuma bayan ya baro tawagar ta Sifaniya, Martinez ya dawo ƙungiyarsa ta Barcelona, inda ya buga wasan da suka yi nasara kan Osasuna a ranar Alhamis.
Shafin Goal ya ambato wata jaridar wasanni ta Sifaniya, Diario Sport, na cewa Osasuna na duba yiwuwar shigar da ƙorafi kan Barcelona saboda zargin taka dokar FIFA dangane da saka ɗan wasan da ya baro tawagar ƙasarsa.
Osasuna na ganin cewa, bai kamata a ce Martinez ya buga wasan ba saboda dokar FIFA ta ce ‘yan wasan da suka baro tawagar ƙasarsu ba za su buga wa ƙungiyarsu wasa ba har sai bayan aƙalla kwanaki biyar, face idan hukumar ƙwallo ta amince masa ya buga
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barcelona
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya janye dokar ta-ɓaci da ya ayyana ta tsawon watanni shida a Jihar Ribas.
Tinubu, ya ayyana dokar tun a ranar 18 ga watan Maris, 2025, saboda rikicin siyasa da ya haifar da tsaiko a harkokin mulki tsakanin ɓangaren Zartarwa da Majalisar Dokokin jihar.
NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025 Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyiA jawabin da ya gabatar a Fadar Shugaban Ƙasa a ranar Laraba, Tinubu ya ce matakin dokar ta-ɓacin ya cimma manufarsa, kuma ba za a tsawaita ba ƙarewar wa’adin da aka gindaya.
“Ina farin ciki yau game da bayanan da ke hannuna, an samu yanayin fahimta a tsakanin dukkanin masu ruwa da tsaki a Jihar Ribas domin dawo da mulkin dimokuraɗiyya cikin gaggawa,” in ji Shugaban Ƙasa.
Gwamnan Jihar, Siminalayi Fubara, da mataimakiyarsa Ngozi Nma Odu, tare da ‘yan majalisar dokokin jihar, za su koma kan kujerunsu daga ranar Alhamis, 18 ga watan Satumba, 2025.
Tun da farko, dokar ta-ɓacin ta dakatar da manyan jami’an gwamnati da masu madafun iko na jihar sakamakon rikici da aka daɗe ana yi a jihar.
“Da ban ayyana wannan dokar ta-ɓacin ba, da hakan ya zama babbar gazawa a wajena a matsayina na Shugaban Ƙasa.
“Amma yanzu da zaman lafiya da doka suka wanzu, al’ummar Jihar Ribas za su sake cin moriyar dimokuraɗiyya,” in ji Tinubu.
Ya kuma yi kira ga gwamnoni da majalisun dokokin jihohi na faɗin Najeriya da su ci gaba da wanzar da zaman lafiya da haɗin kai tsakanin ɓangaren zartarwa da na majalisa.
Har ila yau, ya jaddada cewa zaman lafiya da kyakkyawan shugabanci su ne tubalin kawo ci gaban dimokuraɗiyya ga al’umma.