Gobarar daji ta kashe mutum 24 a Koriya ta Kudu
Published: 26th, March 2025 GMT
Aƙalla mutum 24 ne suka rasu a wata gobarar daji mai muni da ta auku a tarihin Koriya ta Kudu baya ga mummunar ɓarna da ta haddasa.
Mukaddashin shugaban ƙasar ya sanar a ranar Laraba cewa wutar dajin ta rabu kashi daban-daban har fiye da goma tun ƙarshen mako, inda ta laƙume wasu yankunan kudu maso gabashin kasar.
Har ila yau, ta kuma tilasta wa kusan mutum 27,000 ƙaurar gaggawa bayan ta datse tituna da kuma na’urorin sadarwa kamar yadda mazauna yankunan da ke neman tsira da rayukansu suka sanar.
Wani jami’in Ma’aikatar Kare Mutane ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa mutum 18 ne suka gamu da ajalinsu sakamakon wutar dajin baya ga waɗanda suka jikkata.
Sai dai daga bisani kafofin watsa labarai ciki har da BBC da CNN sun ruwaito cewa adadin waɗanda suka rasu ya kai 24 a dalilin gobarar.
A wani batun da ya shafi ƙoƙarin kashe wutar kuma wani jirgin sojin Koriya ta Kudun mai saukar ungulu ya faɗi da safiyar nan inda matuƙinsa ya rasu a ƙoƙarin dakile gobarar mai haddasa barna.
Alƙaluman da muhukunta suka fitar sun nuna cewa kimanin mutum 26 ne suka jikkata a dalilin gobarar dajin wadda ta ɗaiɗaita wani wurin bauta mai tsohon tarihi na mabiya addinin Buddha da ake kira Gounsa da ke yankin Uiseong.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Koriya ta Kudu wutar daji
এছাড়াও পড়ুন:
Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
Mutane da dama daga nahiyar Afirka ne suke cikin mutane kimani 50 wadanda suka rasa rayukansu sanadiyyar hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan wani gidan kaso a lardin Sa’ada na kasar Yemen.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran Al-Masirah yana cewa makaman Amurka sun fada kan wani gidan yarin da aka kebewa yan Afrika, kuma yawansu ya kai 115, amma har yanzun ba’a san yawan wadanda suka rasa rayukansu a gidan yari.
Labarin ya kara da cewa har yanzun ma’aikatan agaji suna aikin ceto a wurin, sannan hotunan da suka fara bayyana sun nuna gawaki da dama. Amma Al-Masirah ta bayyana cewa akalla mutane 68 sun rasa rayukansu.