An Yi Gargadi Akan Rushewar Kungiyar Agajin Falasdianwa Ta UNRWA
Published: 14th, March 2025 GMT
Shugaban kungiyar agajin Falasdinawa ta “UNRWA’ wacce MDD ta kafa, ya yi gargadin rushewarta da hakan zai hana Falasdinawa na yanzu samun ilimi, haka nan kuma bayar da kayan agaji da bukatun yau da kullum ga mutane miliyan 6 a Falasdinu.
Shugaban kungiyar Agajin Philippe Lazzarini ya fada wa kamfanin dillancin labarun Faransa cewa; Da akwai hatsari da gaske da kungiyar take fuskanta na rushewa, da hakan zai kara dagula yanayin da al’ummar Falasdinu suke ciki.
Philippe Lazzarini ya kara da cewa; Idan hakan ta faru, to mun sadaukar da falasdinawan da suke rayuwa a wannan lokacin da hana su ilimi.
Tun bayan farmakon Aksa 2023 ne dai HKI da Amurka su ka dauki matakin haramta kungiyar da dakatar da duk wani aiki da ita.
MDD ce dai ta kafa wannan kungiyar domin taimakawa Falasdinawan da kirkirar HKI ya yi sanadiyyar mayar da su ‘yan gudun hijira.
Wasu kasashe da kuma kungiyoyi da dama a duniya sun yi tir da matakin na HKI da kuma Amurka akan wannan kungiya.
Da akwai yaran Falasdinawa 100,000 a cikin Gada kadai da suke karatu a karkashin makarantun kungiyar.
Philippe Lazzarini ya ce, idan aka hana wadannan yaran karatu to mun shuka irin tsattsauran ra’ayi, wanda zai zama babban bala’i.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da jijjiga sakamakon sauya sheƙar da ’yan siyasa daga ɓangarori daban-daban suke yi.
A baya-bayan nan tsallakawar da wasu jiga-jigan jam’iyyun adawa suka yi zuwa Jam’iyyar APC mai mulki ta jawo ɗiga ayar tambaya a kan dalilansu da kuma makomar hamayya a zaɓen 2027.
Hakan dai yana faruwa ne a daidai lokacin da wasu ’yan ƙasar suke kokawa bisa yadda ake gudanar da mulki da kuma yadda wasu manyan ’yan siyasa suke fadi-tashin kafa wata inuwa da suka ce za ta ciro wa talaka kitse a wuta ta hanyar kawar da gwamnatin APC.
NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin ArewaWannan shi ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai da nufin gano alƙiblar da siyasar Najeriya take shirin fuskanta.
Domin sauke shirin. Latsa nan