Aminiya:
2025-07-09@07:47:52 GMT

DAGA LARABA: Asalin Tashe Da Tarihinsa A Ƙasar Hausa?

Published: 12th, March 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Bayan ɗimbin falala da yawan samuwar ibadun da ke ƙara kusanta bayi ga Ubangijinsu, da azumin watan Ramadan ke zuwa da shi kamar yadda malamai suka saba faɗa, Hakazalika kuma a watan na zuwa da wata al’ada mai ɗimbin tarihi da ke ɗebe wa al’umma musamman na Arewacin Najeriya kewa.

Wannan al’adar ita ce ta tashe da ake fara d zarar watan azumi ya kai kwanaki 10.

DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi

Maza da mata na gudanar da wannan al’ada ta hanyar yin shigar kwaikwayo tare da ɓatar da kama, su ringa zagayawa gidaje da kwararo-kwararo ɗauke da ganga da kayan kaɗe-kaɗe suna bugawa suna waƙa.

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba ne kan wannan daɗaɗɗiyar al’adar, don jin inda ta samo asali, tarihinta da kuma yadda ake gudanar da ita.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hausawa Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa

An sake gudanar da wani sabuwar zanga-zanga a manyan biranen duniya domin neman kawo karshen kisan kiyashin da ake yi a Gaza

A jiya asabar ne aka sake gudanar da wata sabuwar zanga-zanga a kasashe da dama na duniya domin nuna adawa da hare-haren da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ke ci gaba da kai wa kan zirin Gaza, wanda ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa sama da 192,000 tare da jikkata yawancinsu mata da kananan yara.

A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, mutane da dama ne suka gudanar da zanga-zanga a gaban ma’aikatar harkokin wajen kasar a Quito babban birnin kasar, domin nuna goyon bayansu ga Falasdinawa a zirin Gaza.

Masu zanga-zangar sun yi kira da a kawo karshen yaki da kisan kare dangi a Gaza. Sun daga tutocin Falasdinawa da tutocin nuna kyamar yaki, yayin da wasu ke dauke da jajayen fulawa da aka lullube da fararen fulawa, wanda ke nuna alamar girmamawa ga yaran Gaza da aka kashe.

A Faransa, masu zanga-zangar sun yi maci a kan titunan birnin Paris, suna neman kawo karshen kisan kiyashin da gwamnatin mamayar Isra’ila ke ci gaba da yi kan al’ummar Falasdinu.

Masu zanga-zangar sun yi Allah wadai da rashin mutunta dokokin kasa da kasa tare da yin kira ga kasashen yamma karkashin jagorancin Faransa da su kakaba wa gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila takunkumi mai tsanani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kaso 90 na ’yan bindigar da suka addabi Katsina ’yan asalin jihar ne – Radda
  • DAGA LARABA: Shin Ko Zafin Nema Na Kawo Samu?
  • ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
  • Mata Da Matasa Dari Hudu Suka Amfana Da Tallafi A Gandun Albasa Kano
  • NAJERIYA A YAU: Sarkakiyar Dake Gaban Hadakar ADC — Atiku Ko Peter Obi
  • Miliyoyin Yan Najeriya Ne Suka Gudanar da Tattakin Ashoora Wasu Kuma A Makarantunsu…
  • NAJERIYA A YAU: Mene ne tasirin naɗin Mataimaka na Musamman a rayuwar jama’a?
  • Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko
  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala
  • Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa