Allah Ya yi wa babban malamin Musulunci a Najeriya Sheikh Sa’idu Hassan Jingir rasuwa, bayan fama da rashin lafiya.
Marigayi Sheikh Sa’idu Hassan Jingir shi ne Mataimakin Shugaban Majalisar Malamai na II na Ƙasa Ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bida Wa Iqamatis Sunan (JIBWIS).
Ana sa rana gudanar jana’izarsa da misalin ƙarfe biyu 2:00 na rana a Masallacin Santa, Unguwar Rimi cikin birnin Jos.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
Isra’ila ta ce mutum takwas sun mutu a daren ranar Litinin sakamakon sabon harin da Iran ta kai a biranen Tel Aviv da Haifa da wasu sassa na ƙasar.
Wannan na zuwa ne a matsayin ci gaba daga jerin hare-hare da Iran ke kai wa tun bayan da Isra’ila ta fara kai mata hari makonnin da suka wuce.
NAJERIYA A YAU: Dalilan Durƙushewar Sababbin Sana’o’i Tun Ba A Je Ko’ina Ba Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da HaifaYanzu haka, adadin mutanen da hare-haren Iran suka kashe a Isra’ila ya kai 24, yayin da mutane sa.a da 300 ke kwance a asibitoci saboda raunuka.
Isra’ila ta ce a martaninta, jiragen yaƙin ƙasar sun kai hari a birnin Tehran, babban birnin Iran, inda suka lalata wata hedikwatar dakarun juyin juya hali.
Haka kuma sun kai farmaki a wasu cibiyoyi da Iran ke adana makamai a tsakiyar ƙasar.
An fara wannan rikici ne bayan da Isra’ila ta kai hari da asubahin ranar Juma’a a Iran.
Iran ta ce a wannan harin, mutane sama da 200 ne suka mutu.
Wannan hari ya fusata gwamnatin Iran, inda ta fara mayar da martani da hare-hare a Isra’ila.
A baya ma, ana zargin Isra’ila da kai hare-hare da dama a Iran, musamman kan dakarun da ta ke zargi da taimaka wa ƙungiyoyin da ke barazana gare ta, kamar Hezbollah da Hamas.
Rikicin ya ci gaba da tsananta, yayin da kowane ɓangare ke kai farmaki ga ɗaya, al’ummar ƙasashen biyu na ci gaba da jikkata da mutuwa.