Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha
Published: 2nd, March 2025 GMT
Mijin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, Emmanuel Oritsejolomi Uduaghan, ya bayyana cewa matarsa ta taɓa kawo masa ƙorafi game da cin zarafin da ta ce Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya yi mata.
A cewarsa, rikicin ya fara tun lokacin da Natasha ta tsaya takarar kujerar Sanata a 2019 a ƙarƙashin jam’iyyar SDP, inda ta nemi kujerar Sanatan Kogi ta Tsakiya.
A lokacin, Akpabio yana riƙe da mukamin Ministan Neja Delta.
“Da kaina na je na same shi na buƙaci ya bai wa matata girman da ta cancanta, sannan ya girmama abotar da ke tsakaninmu.
“Bayan mun tattauna sai muka amince da a warware maganar cikin mutunci,” in ji shi.
Bayan zaɓen 2019, Natasha ta sake tsayawa takarar Sanata a 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, inda ta samu nasara.
A lokacin, ana raɗe-raɗin cewa Akpabio bai ji daɗin yadda ta samu goyon baya ba, kuma hakan ya ƙara haddasa rashin jituwa a tsakaninsu.
“Amma bayan maganar da muka yi, sai matata ta ci gaba da bayyana damuwa game da irin cin zarafin da ta ke fuskanta daga shugaban majalisar.
“Ni dai na yarda da matata, kuma aure muka yi na soyayya da ƙauna. Babu abin da ya fi min ita a yanzu domin ita ce farin cikina.”
Natasha dai ta ce tana da wasu hujojji da za ta fitar, wanda ke nuna yadda Akpabio ya neme ta, lamarin da yanzu haka ya haifar da zazzafar muhawara a Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cin zarafi Majalisar Dattawa Muhawara Siyasa zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Saboda wannan baiwa daga Allah, iyalai da ‘yan uwan mai akuyar suka sanar da shirye-shiryen gudanar da bikin murnar haihuwar ‘ya’yan akuyar a ranar Lahadi mai zuwa a Garun Dakasoye, karamar hukumar Garun Malam ta Jihar Kano, inda za a yi musu suna da kuma karatun Alkur’ani mai girma.
A nasa bangaren, mahaifin budurwar, Malam Aliyu dake Garin Dakasoye, ya tabbatar da cewa za su gudanar da bikin domin nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki bisa wannan ni’ima da ya ba su.
Ya kara da cewa: “Mun gode wa Allah bisa wannan arziki, kuma muna sa ran gudanar da bikin tare da sanya musu suna domin nuna godiya ga Allah mai daukaka.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp