Girmama Hukuncin Kotu Muhimmin Jigo Ga Dimokuradiyya – Farfesa Fagge
Published: 22nd, February 2025 GMT
An shawarci shugabanni da aka zaba da su girmama hukuncin kotu domin tabbatar da dimokuradiyya a ƙasar.
Wani malami a Jami’ar Bayero ta Kano, Farfesa Kamilu Fagge, ya bayar da wannan shawara a Kaduna, yana nuna damuwarsa kan zargin karya dokokin kotu a harkokin siyasa.
Ya bayyana damuwarsa kan matakin da Gwamna Ademola Adeleke na Jihar Osun ya dauka na gudanar da zaɓen kananan hukumomi duk da umarnin kotu da ke hana hakan.
Farfesa Fagge ya gargaɗi shugabanni da aka zaɓa cewa rashin mutunta hukuncin kotu, duk da rantsuwar da suka yi na kare kundin tsarin mulkin ƙasa da bin doka, na iya zama barazana ga dimokuradiyya.
SULEIMAN KAURA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Dimokuradiyya Farfesa Fagge
এছাড়াও পড়ুন:
An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Binciken likitoci da ‘yansanda ya tabbatar cewa gubar ce ta yi sanadin mutuwarsa.
Haka kuma, kotun ta yanke wa wani mutum mai suna Sani Sa’adu hukuncin ɗaurin shekara biyar saboda ɓoye gaskiya da ya yi dangane da wata Gift Bako, wadda ake zargi da hannu a kisan.
Lauyoyin waɗanda aka yanke wa hukunci sun nemi sassauci saboda suna da iyalai, amma lauyan gwamnati ya bayyana jin daɗinsa da hukuncin, inda ya ce an yi adalci kamar yadda doka ta tanada.
Rabe Nasir, ya taɓa zama ɗan majalisar tarayya da kuma kwamishinan Jihar Katsina a lokacin mulkin tsohon gwamnan jihar Aminu Bello Masari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp