Leadership News Hausa:
2025-11-02@18:11:14 GMT

Sadaukantaka, Kunya Da Kawar Da Kai Na Annabi Muhammadu (SAW)

Published: 21st, February 2025 GMT

Sadaukantaka, Kunya Da Kawar Da Kai Na Annabi Muhammadu (SAW)

Annabi (SAW) yana da Alfadarai Bakwai, akwai wazanda ya rike har ya rasu suna wurinsa akwai kuma wazanda ya bai wa wasu daga cikin sahabbansa. Wacce ya je yakin Hunaini da ita, wani sarkin Larabawa (zan makafatul kinani) ne ya bashi, akwai wacce sarkin Ailatu ya bashi akwai ta sarkin Limatul Jandali, akwai ta Sarki Najjashi, akwai ta sarkin Kisra, akwai ta sarkin Mukaukisu akwai Jindilu.

Jindilu itace mashhuriya wacce Annabi ya rasu ya bar ta Sayyidina Aliyu ya ci gaba da hawanta, duk yakukuwan Sayyidina Ali, mafi yawancinsu a kanta ya yi, ranar yakin Wak’atu Jamal, Sayyada A’isha (RA) ta ganshi a kanta, sai ta ce “ya yi kama da zan’uwansa” sai mai rike da akalar rakuminta ya jefar ya koma cikin rundunar Sayyadina Ali ya ce masa, Sayyada tace “ka yi kama da zan’uwanka (Sayyadina Rasulallah).

Imam Muslim ya ruwaito Hadisi daga Abbas yana cewa “yayin da tawagar Musulmai da Kafirai suka hazu, sai Musulmai suka gudu suka juya baya, sai Manzon Allah shi kuma ya kasance yana jan alfadarinsa inda Kafiran suke, ni kuma ina rike da linzamin alfadarinsa ina jan linzamin baya shi kuma Abu Sufyan zan Haris zan Abdulmuzallib yana rike da wurin sanya kafafuwa na shimfizar alfadarin, sannan Annabi (SAW) ya yi kira ga Musulmai suka dawo.” A wata ruwaya kuma, Annabi (SAW), Baffansa Abbas ya sa ya kira Musulmai.

Annabi (SAW) ya kasance idan ya yi fushi (shi kuma ba ya fushi sai in an taba Allah), to wani abu bai iya tare shi, ko Sahabi ko tsoro ko wata razana.

Abdullahi zan Umar ya ce, “ban taba ganin wani abu mafi sadaukantaka ko karfin zuciya ko kyauta mafi yarda wanda ya fi Annabi (SAW) ba.”

Sayyadina Ali yana cewa “Mun kasance in yaki ya yi zafi, ya yi tsanani idanuwa suka sauya kala suka yi ja, sai mu dinga kare kanmu da Annabi (SAW), babu wani da yake kusantar makiya sai shi, sannan mu biyo bayansa.

An karbo Hadisi daga Anas yana cewa “Manzon Allah (SAW) ya kasance mafi kyawun Mutane, mafi kyautar mutane, mafi sadaukantakar mutane.”

Wata rana da dare mutanen Madina sun razana sabida kara mai karfi da aka ji ta taso a daren, Sahabbai suka fara bi gida-gida suna taso abokansu a je a duba sabida a san me ke faruwa. Kawai sai suka hazu da Manzon Allah (SAW) yana dawowa, ya riga su zuwa wurin, sabida sauri a dokin Abi Dalhata ya je kuma babu shimfiza a kan dokin, yana rataye da takobi yana cewa Sahabbai “kar ku tsorata, na je na gani babu komai.”

A wannan lokaci Madina ta kasance kullum ana tsoron wani daga cikin Sarakunan makiya zai kawo hari.

Imran bin Hussaini yake cewa, Manzon Allah (SAW) bai taba hazuwa da wata runduna ba sai ya kasance na farko wanda zai fara kai musu hari.

Yayin da Ubayyu bin Khalaf ya ga Annabi (SAW) a ranar yakin Uhudu, Ubayyu ya fito yana cewa, Ina Muhammadu yau sai zaya ya mutu a cikinmu, ko ni ko shi. Ubayyu yana daga cikin wazanda suka fanshi kansu a ranar yakin Badr, bayan ya fanshi kanshi sai ya ce wa Annabi (SAW), yana da doki da ya kulle kullum yana bashi masaki na dawa, a kansa zan kashe ka, sai Manzon Allah (SAW) ya ce masa, Insha Allah, ni ne zan kashe ka a kanshi. A ranar yakin Uhudu da Ubayyu ya ga Annabi (SAW), sai ya sukwano dokinshi zuwa ga Annabi (SAW), Mazaje sadaukai suka yi kanshi sai (SAW) ya ce musu “ku kyale shi haka nake so”. Sai Manzon Allah (SAW) ya karbi wani mashi a hannun wani sahabi sannan ya soke shi a wuya daga kan dokinshi, sai ya koma yana ce wa kuraishawa, Muhammadu ya kashe ni, an ruwaito cewa, Ubayyu ya Mutu a hanyar dawowarsa daga Uhudu zuwa Makkah.

Kunya Da Kawar Da Kai Na Manzon Allah (SAW)

Wannan kazan kenan daga cikin sadaukantaka irin ta Annabi (SAW), yanzun kuma za mu juya akalar karatunmu zuwa ambaton wasu daga cikin halayen Kunya da kawar da kai na Manzon Allah (SAW).

Abin da ake nufi da kunya shi ne taushin zuciya da yake bijirowa a fuskar zan Adam yayin da mutum ya aikata wani aiki ko ya faza wata magana da ake kin ji ko gani, ko kuma mutum ya aika ta abin da rashin aikata shi ya fi, sai zan Adam ya ce “ina ma na bari ban aikata ba.”

Shi kuma runtse ido ko kawar da kai, yana nufin rafkana da abin da mutum ba ya so a aikata masa (ba ya so a aikata masa wani abu, ga kuma wani ya nace sai ya aikata abin da ba a son) shi kuma sai ya kawar da kai ya nuna bai san ma ana yi ba.

Manzon Allah (SAW) ya fi kowa Kunya sabida Hadisin “Alhaya’u minal Iman… – Kunya tana daga cikin Imani”.

Manzon Allah (SAW) yana cewa, “wanda bai da kunya, ya aikata abin da ya ga dama, Allah ba ruwanshi da shi”. Annabi (SAW) shi ne mafi kawar da kai ga Al’aurar Mutane.

Ubangiji tabaraka wata’ala ya faza cikin kur’ani “Ya ayyuhallazina amanu la tadkhulu buyutan nabiyya illa an yu’uzana lakum ila za’amin gaira nazirina inahu…”

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kunya kawar da kai ranar yakin

এছাড়াও পড়ুন:

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

“Haka kuma an kama wata mata mai shekaru 34 da ake zargi da hannu a lamarin, tare da wasu masu gidan marayu guda biyu da ke Abuja da Jihar Nasarawa, inda aka gano wasu yaran da ake kyautata zaton an yi safarar su. Wasu daga cikin gidajen marayun da aka gano ana amfani da su ne a matsayin cibiyoyin ajiye yara, inda ake jiran ‘kwace’ ko sayar da su da sunan daukar nauyin marayu.”

Ya ce, “An gano gidajen marayu guda hudu da ke Kaigini, Kubwa Edpressway Abuja; Masaka Area 1, Mararaba kusa da Abaca Road; da kuma Mararaba bayan Kasuwar Duniya suna da alaka da wannan kungiya, kuma ana ci gaba da bincike a kansu.”

Ya kara da cewa, daya daga cikin masu korafin ya bayyana cewa ya biya Naira miliyan 2.8 a matsayin kudin daukar yaro, sannan ya biya Naira 100,000 a matsayin kudin shawara ga daya daga cikin ‘yan kungiyar.

Sanarwar ta kara da cewa, “Wani mai korafi ya ce shi ma ya biya Naira miliyan 2.8 kudin daukar yaro da Naira 100,000 kudin shawara ga wani dan kungiyar.

“An canza sunayen yawancin yaran da aka ceto, lamarin da ya kara wahalar da bincike da gano asalinsu,” in ji sanarwar.

Darakta Janar ta NAPTIP, Binta Adamu Bello, ta bayyana damuwarta kan wannan lamari, inda ta ce safarar yara ta zama babbar matsala a kasa.

Ta hanyar Adekoye, DG din ta nuna damuwa game da yadda wasu gidajen marayu ke amfani da raunin jama’a wajen aiwatar da safarar yara.

Ta ce, “Abin takaici ne yadda wasu masu mugunta da ke da sunayen kwararru da matsayi a cikin al’umma, suke amfani da matsayin su wajen yaudarar mutanen da ke cikin mawuyacin hali, su yi safarar ‘ya’yansu, da dama daga cikinsu ma sun tsira ne daga halaka a lokacin rikice-rikicen al’umma ko na manoma da makiyaya, sannan a sayar da su ga iyaye masu neman haihuwa a matsayin daukar yaro ba tare da sahihin izinin iyayensu ba.

“Wannan abin ba za a yarda da shi ba, kuma wadanda aka kama kan wannan mugun aiki za su fuskanci hukuncin doka yadda ya kamata.

“’Ya’yanmu ba kayayyaki ba ne da za a ajiye su a gidajen marayu a sayar ga mai biyan mafi tsada. Wannan dole ya tsaya,” in ji ta.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa November 1, 2025 Manyan Labarai Jerin Gwarazan Taurarinmu November 1, 2025 Manyan Labarai Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Maganin Nankarwa (3)
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
  • Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu