Sadaukantaka, Kunya Da Kawar Da Kai Na Annabi Muhammadu (SAW)
Published: 21st, February 2025 GMT
Annabi (SAW) yana da Alfadarai Bakwai, akwai wazanda ya rike har ya rasu suna wurinsa akwai kuma wazanda ya bai wa wasu daga cikin sahabbansa. Wacce ya je yakin Hunaini da ita, wani sarkin Larabawa (zan makafatul kinani) ne ya bashi, akwai wacce sarkin Ailatu ya bashi akwai ta sarkin Limatul Jandali, akwai ta Sarki Najjashi, akwai ta sarkin Kisra, akwai ta sarkin Mukaukisu akwai Jindilu.
Imam Muslim ya ruwaito Hadisi daga Abbas yana cewa “yayin da tawagar Musulmai da Kafirai suka hazu, sai Musulmai suka gudu suka juya baya, sai Manzon Allah shi kuma ya kasance yana jan alfadarinsa inda Kafiran suke, ni kuma ina rike da linzamin alfadarinsa ina jan linzamin baya shi kuma Abu Sufyan zan Haris zan Abdulmuzallib yana rike da wurin sanya kafafuwa na shimfizar alfadarin, sannan Annabi (SAW) ya yi kira ga Musulmai suka dawo.” A wata ruwaya kuma, Annabi (SAW), Baffansa Abbas ya sa ya kira Musulmai.
Annabi (SAW) ya kasance idan ya yi fushi (shi kuma ba ya fushi sai in an taba Allah), to wani abu bai iya tare shi, ko Sahabi ko tsoro ko wata razana.
Abdullahi zan Umar ya ce, “ban taba ganin wani abu mafi sadaukantaka ko karfin zuciya ko kyauta mafi yarda wanda ya fi Annabi (SAW) ba.”
Sayyadina Ali yana cewa “Mun kasance in yaki ya yi zafi, ya yi tsanani idanuwa suka sauya kala suka yi ja, sai mu dinga kare kanmu da Annabi (SAW), babu wani da yake kusantar makiya sai shi, sannan mu biyo bayansa.
An karbo Hadisi daga Anas yana cewa “Manzon Allah (SAW) ya kasance mafi kyawun Mutane, mafi kyautar mutane, mafi sadaukantakar mutane.”
Wata rana da dare mutanen Madina sun razana sabida kara mai karfi da aka ji ta taso a daren, Sahabbai suka fara bi gida-gida suna taso abokansu a je a duba sabida a san me ke faruwa. Kawai sai suka hazu da Manzon Allah (SAW) yana dawowa, ya riga su zuwa wurin, sabida sauri a dokin Abi Dalhata ya je kuma babu shimfiza a kan dokin, yana rataye da takobi yana cewa Sahabbai “kar ku tsorata, na je na gani babu komai.”
A wannan lokaci Madina ta kasance kullum ana tsoron wani daga cikin Sarakunan makiya zai kawo hari.
Imran bin Hussaini yake cewa, Manzon Allah (SAW) bai taba hazuwa da wata runduna ba sai ya kasance na farko wanda zai fara kai musu hari.
Yayin da Ubayyu bin Khalaf ya ga Annabi (SAW) a ranar yakin Uhudu, Ubayyu ya fito yana cewa, Ina Muhammadu yau sai zaya ya mutu a cikinmu, ko ni ko shi. Ubayyu yana daga cikin wazanda suka fanshi kansu a ranar yakin Badr, bayan ya fanshi kanshi sai ya ce wa Annabi (SAW), yana da doki da ya kulle kullum yana bashi masaki na dawa, a kansa zan kashe ka, sai Manzon Allah (SAW) ya ce masa, Insha Allah, ni ne zan kashe ka a kanshi. A ranar yakin Uhudu da Ubayyu ya ga Annabi (SAW), sai ya sukwano dokinshi zuwa ga Annabi (SAW), Mazaje sadaukai suka yi kanshi sai (SAW) ya ce musu “ku kyale shi haka nake so”. Sai Manzon Allah (SAW) ya karbi wani mashi a hannun wani sahabi sannan ya soke shi a wuya daga kan dokinshi, sai ya koma yana ce wa kuraishawa, Muhammadu ya kashe ni, an ruwaito cewa, Ubayyu ya Mutu a hanyar dawowarsa daga Uhudu zuwa Makkah.
Kunya Da Kawar Da Kai Na Manzon Allah (SAW)
Wannan kazan kenan daga cikin sadaukantaka irin ta Annabi (SAW), yanzun kuma za mu juya akalar karatunmu zuwa ambaton wasu daga cikin halayen Kunya da kawar da kai na Manzon Allah (SAW).
Abin da ake nufi da kunya shi ne taushin zuciya da yake bijirowa a fuskar zan Adam yayin da mutum ya aikata wani aiki ko ya faza wata magana da ake kin ji ko gani, ko kuma mutum ya aika ta abin da rashin aikata shi ya fi, sai zan Adam ya ce “ina ma na bari ban aikata ba.”
Shi kuma runtse ido ko kawar da kai, yana nufin rafkana da abin da mutum ba ya so a aikata masa (ba ya so a aikata masa wani abu, ga kuma wani ya nace sai ya aikata abin da ba a son) shi kuma sai ya kawar da kai ya nuna bai san ma ana yi ba.
Manzon Allah (SAW) ya fi kowa Kunya sabida Hadisin “Alhaya’u minal Iman… – Kunya tana daga cikin Imani”.
Manzon Allah (SAW) yana cewa, “wanda bai da kunya, ya aikata abin da ya ga dama, Allah ba ruwanshi da shi”. Annabi (SAW) shi ne mafi kawar da kai ga Al’aurar Mutane.
Ubangiji tabaraka wata’ala ya faza cikin kur’ani “Ya ayyuhallazina amanu la tadkhulu buyutan nabiyya illa an yu’uzana lakum ila za’amin gaira nazirina inahu…”
কীওয়ার্ড: Kunya kawar da kai ranar yakin
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
Aƙalla masallata 40 ’yan bindiga suka sace a wani masallaci da ke Gidan Turbe a Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara da safiyar wannan Litinin.
Majiyoyi sun ce an yi awon gaba da masallatan ne zuwa dazukan Gohori da ke yankin Tsafe.
Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a LegasWannan harin dai kai tsaye masu ruwa da tsaki na kallonsa a matsayin kawo ƙarshen yarjejeniyar sulhu tsakanin ’yan bindigar da mahukuntan jihohin Zamfara da Katsina.
A baya-bayan nan ne jihohin Katsina da Zamfara suka ƙulla yarjejeniyar sulhu tsakaninsu da ’yan bindigar da suka addabi al’ummar jihohin arewa maso yammacin Najeriyar.
Yarjejeniyar sulhu da aka cimma a dajin Wurma ta samu halartan manyan ’yan bindiga irinsu Alhaji Usman Kachalla Ruga da Muhindinge da Yahaya Sani ( Hayyu ) da kuma Shu’aibu.
A ɓangaren mahukunta, akwai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi da kuma shugaban ƙaramar hukuma Babangida Abdullahi Kurfi.
’Yan bindiga sun saki wasu mutane da suke garkuwa da su a lokacin yarjejeniyar sulhun, tare da barin al’umma zuwa gonakinsu ba tare da wata fargaba ko tsangwama.
To sai dai kuma, ƙasa da wata guda bayan cimma wannan yarjejeniya, rahotanni sun ce ’yan bindiga sun kutsawa wani ƙauye a Zamfara tare da awon gaba da masallata.
Shaidun gani da ido sun ce, maharan sun yi wa masallacin ƙawanya da misalin ƙarfe 5:30 na safe, daidai lokacin da jama’a ke sallar asuba.