Gwamnatin Niger Ta Hana Yan Najeriya Dauke Da Passpor Ta Na ECOWAS Shiga Kasar
Published: 19th, February 2025 GMT
Gwamnatin Jumhuriyar Nijer daga jiya Talata ta fara aikin hana yan Najeriya dauke da Passport na kungiyar ECOWAS shiga kasar.
Kafin haka dai mutane daga kasashen ECOWAS suna shiga kasashen kungiyar ba tare da bukatar visar shiga ko wace kasa daga cikin kasashe kungiyar ba.
Amma bayan da kasashe 3 Nijer, Burkina Faso da kuma Mali suka fice daga kungiyar sannan suka samar da sabon Passport a tsakanin kasashen uku, sai al-amura suka fara sauyi tsakaninu da Ecowas.
Sun fara hana wadanda suke rike da Passpory na kasashen ECOWAS shiga kasashen ba tare da visa ba.
Gwamnatin Nijer bata bada sanarwan fara aiki da wannan dokar ba. Kuma wani jami’in shige da fice na Niger ya ce umurnin ne aka basu.
A bangaren Najeriya kuma gwamnatin kasar ta ce bata da masaniyya dangane da hakan. Amma za ta fara bincike don tabbatar da yadda al-amarin yake.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Babu wanda ya tsira daga hatsarin Jirgin Air India mai dauke da fasinjoji 242
Hukumomi a India sun ce da yiwa a samu wanda ya tsira daga hatsarin jirgin samanAir India da ya faru a yau Alhamis.
Jirgin samfarin Boeing 787 Dreamliner wanda ya tashi Ahmedabad zuwa birnin Landan ya yi hatsari jim kadan bayan tashinsa dauke da fasinjoji 242 da ma’aikatan jirgin inji kamfanin air India.
Bayanan farko da kamfanin na Indiya ya fitar sun ce akwai, Indiyawa 169, ‘yan Burtaniya 53 da, ‘yan Portugal 7 sai dan Canada guda a cikin jirgin. Kuma babu wanda ya tsira, a cewar shugaban ‘yan sandan Ahmedabad.
Hukumomin India da na Ingila da Portigal duk sun jajanta game da mummunan hatsarin.
Jami’an kashe gobara a arewa maso yammacin Indiya tun da farko sun shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa wani jirgin sama ya fado a filin jirgin.
Hotunan farko da aka watsa a gidajen talabijin na Indiya sun nuna wani jirgin sama yana shawagi a wata unguwa, kafin ya bace wurin ya turnuke da bakin hayaki.
Bayanai sun ce wannan shi ne hatsarin farko na jirgin Boeing 787 Dreamliner wanda ya fara aiki a shekarar 2011.
Kamfanin Boeing ya ce tuni ya fara tattara bayanai don sanin hakikanin abinda ya faru.