Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Hadu Da Fushin ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinawa
Published: 14th, February 2025 GMT
‘Yan gwagwarmayar Falasdinawa suna ci gaba da mayar da martini kan hare-haren wuce gona da iri da sojojin mamayar Isra’ila suke kai wa kan gabar yammacin kogin Jordan
Sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da kai farmakin soji a cikin dare da safiyar kan garuruwan da suke gabar yammacin kogin Jordan, inda sojojin mamayar suka kaddamar da munanan hare-hare a kan sansanin Jenin sannan wani jirgin yakin haramtacciyar kasar Isra’ila ya yi luguden bama-bamai kan gidajen Falasdinawa.
A halin da ake ciki kuma, Bataliyar Nablus da ke karkashin Sarayal-Quds na kungiyar Jihadul-Islami ta sanar da kai wa sojojin mamayar Isra’ila hari da harsasai da tada bama-bamai, yayin da dakarun shahidan Al-Aqsa suka tabbatar da gwabza kazamin fada da sojojin mamayar haramtacciyar kasar Isra’ila.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: sojojin mamayar Isra ila da sojojin mamayar
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
A yayin samamen, kakakin ‘yansandan Neja ya ce an kama mutane shida a wurin da ake hakar ma’adinan yayin da wasu kuma suka tsere.
Abiodun ya bayyana sunayen wadanda ake cafken da Aliyu Rabiu, Samaila Ibrahim, Sadiku Auwal, Ibrahim Babangida, Musa Adamu da Sani Hassan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp