Aminiya:
2025-09-18@00:57:17 GMT

Kotu ta yanke hukuncin sare hannun matashi kan sare hannun yaro a Gombe

Published: 13th, February 2025 GMT

Babbar Kotun Jiha ta 5 a Gombe, ƙarƙashin Jagorancin Mai Shari’a A.M. Haruna, ta yanke wa wani matashi mai suna Abdullahi Suleiman hukuncin sare masa hannu, bisa samunsa da laifin sare hannun wani yaro mai suna Khalifa Abubakar, ɗan shekara 14 da adda.

Lamarin ya faru ne a ranar 12 ga watan Fabrairu, shekarar 2022, a garin Moddibo da ke Ƙaramar hukumar Yamaltu Deba, a jihar ta Gombe lokacin wani bikin aure da ya rikiɗe ya koma rikici da misalin ƙarfe 11 na dare yayin da angon ya kori duk wanda ke wajen saboda hayaniyar da ta kaure.

Ba zan daina sukar gwamnatin Tinubu ba — Farfesa Yusuf Sojoji sun doki ’yan sanda kan kama ‘mai laifi’

A lokacin fitar jama’a daga wajen bikin, Abdullahi Suleiman, wanda ya fito daga ƙauyen Wajari, ya yi amfani da adda wajen tarwatsa jama’a tare da wasu matasa.

Khalifa Abubakar, wanda takalminsa ya faɗi a wajen gudu, ya tsaya don ɗauka, amma Abdullahi ya kai masa sara da adda har ya sare masa hannun dama gaba ɗaya.

’Yan uwan Khalifa sun gaggauta kai shi Asibitin Koyarwa na Gwamnatin Tarayya da ke Gombe, inda aka masa jinya bayan sare masa hannun.

Bayan faruwar lamarin, ‘yan uwan Khalifa sun kai ƙara ofishin ‘yan sanda da ke Deba. Sai dai daga baya an ba da belin Abdullahi Suleiman. Wannan ya sa gwamnati ta shiga lamarin, inda lauyan gwamnati, Barista Y.G. Ahmad, ya shigar da ƙara a gaban Babbar Kotun Jiha ta 5. Karar mai lamba GM/88c / 2022

A yayin shari’ar, kotun ta saurari shaidu biyar daga ɓangaren mai ƙara, ciki har da Khalifa Abubakar, waɗanda suka tabbatar cewa Abdullahi Suleiman ne ya aikata laifin.

Daga cikin shaida uku, sun kasance shaidun gani da ido da suka tabbatar da cewa Abdullahi ne ya sari Khalifa a lokacin rikicin.

Likitan da ya duba Khalifa shi ma Kotu ta gayyato shi ya bada shaidar jinyar da ya yi masa.

A ɓangaren wanda ake kara kuwa shaidu biyu ya gabatar wa kotu amma ba su bayar da hujjoji masu ƙarfi ba. inda bayan tantance shaidun, kotu ta tabbatar da laifin da ake tuhumar Abdullahi Suleiman akai.

Bayan tabbatar da laifin, kotu ta yi la’akari da yadda Abdullahi Suleiman ya nemi afuwa tare da nuna nadama. Sai dai Lauyan sa, Y.A. Waziri, ya roƙi kotu ta amince su saya wa Khalifa hannun roba, amma kotu ta ƙi yarda da wannan roƙo.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Koto sare hannun matashi Yamaltu Deba

এছাড়াও পড়ুন:

Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi

Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Saudiyya na iya taka muhimmiyar rawa wajen hadin kan kasashen musulmi

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Gwamnatin sahayoniyya ba za ta kuskura ta kai hari ko kai wa wata kasa ta Musulunci hari ba matukar kasashen musulmi suka hade kansu; kuma Saudiyya za ta iya taka muhimmiyar rawa a tafarkin hadin kan kasashen musulmi.

A yayin ganawarsa da yarima mai jiran gado na Saudiyya Mohammed bin Salman a gefen taron Doha, Pezeshkian ya bayyana jin dadinsa da yadda dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ke kara bunkasa, yana mai cewa: Zurfafa da karfafa hadin gwiwar dake tsakanin kasashen Iran da Saudiyya zai kare muradun kasashen biyu, da kuma muradun al’ummomin kasashen biyu, da kuma moriyar al’ummomin kasashen musulmi a yankin.

Pezeshkian ta ci gaba da cewa, alhakin da ke wuyan manyan kasashen musulmi ciki har da Saudiyya a halin da ake ciki a halin yanzu yana da nauyi, ya kuma kara da cewa: Idan kasashen musulmi suka hade kansu, to kuwa gwamnatin sahayoniyya ba za ta kuskura ta kai hari ko mamaye wata kasa ta musulmi ba, Saudiyya za ta iya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da hadin kan kasashen musulmi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan   September 16, 2025 Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida September 16, 2025 Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya September 16, 2025 An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna September 16, 2025 Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza September 16, 2025 Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A  HKI September 16, 2025 Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Ministan Tsaron Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha