Kotu ta yanke hukuncin sare hannun matashi kan sare hannun yaro a Gombe
Published: 13th, February 2025 GMT
Babbar Kotun Jiha ta 5 a Gombe, ƙarƙashin Jagorancin Mai Shari’a A.M. Haruna, ta yanke wa wani matashi mai suna Abdullahi Suleiman hukuncin sare masa hannu, bisa samunsa da laifin sare hannun wani yaro mai suna Khalifa Abubakar, ɗan shekara 14 da adda.
Lamarin ya faru ne a ranar 12 ga watan Fabrairu, shekarar 2022, a garin Moddibo da ke Ƙaramar hukumar Yamaltu Deba, a jihar ta Gombe lokacin wani bikin aure da ya rikiɗe ya koma rikici da misalin ƙarfe 11 na dare yayin da angon ya kori duk wanda ke wajen saboda hayaniyar da ta kaure.
A lokacin fitar jama’a daga wajen bikin, Abdullahi Suleiman, wanda ya fito daga ƙauyen Wajari, ya yi amfani da adda wajen tarwatsa jama’a tare da wasu matasa.
Khalifa Abubakar, wanda takalminsa ya faɗi a wajen gudu, ya tsaya don ɗauka, amma Abdullahi ya kai masa sara da adda har ya sare masa hannun dama gaba ɗaya.
’Yan uwan Khalifa sun gaggauta kai shi Asibitin Koyarwa na Gwamnatin Tarayya da ke Gombe, inda aka masa jinya bayan sare masa hannun.
Bayan faruwar lamarin, ‘yan uwan Khalifa sun kai ƙara ofishin ‘yan sanda da ke Deba. Sai dai daga baya an ba da belin Abdullahi Suleiman. Wannan ya sa gwamnati ta shiga lamarin, inda lauyan gwamnati, Barista Y.G. Ahmad, ya shigar da ƙara a gaban Babbar Kotun Jiha ta 5. Karar mai lamba GM/88c / 2022
A yayin shari’ar, kotun ta saurari shaidu biyar daga ɓangaren mai ƙara, ciki har da Khalifa Abubakar, waɗanda suka tabbatar cewa Abdullahi Suleiman ne ya aikata laifin.
Daga cikin shaida uku, sun kasance shaidun gani da ido da suka tabbatar da cewa Abdullahi ne ya sari Khalifa a lokacin rikicin.
Likitan da ya duba Khalifa shi ma Kotu ta gayyato shi ya bada shaidar jinyar da ya yi masa.
A ɓangaren wanda ake kara kuwa shaidu biyu ya gabatar wa kotu amma ba su bayar da hujjoji masu ƙarfi ba. inda bayan tantance shaidun, kotu ta tabbatar da laifin da ake tuhumar Abdullahi Suleiman akai.
Bayan tabbatar da laifin, kotu ta yi la’akari da yadda Abdullahi Suleiman ya nemi afuwa tare da nuna nadama. Sai dai Lauyan sa, Y.A. Waziri, ya roƙi kotu ta amince su saya wa Khalifa hannun roba, amma kotu ta ƙi yarda da wannan roƙo.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Koto sare hannun matashi Yamaltu Deba
এছাড়াও পড়ুন:
HOTUNA: NDLEA ta ƙone tan dubu 52 na miyagun ƙwayoyi a Zariya
Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), reshen Jihar Kaduna, ta ƙone fiye da tan 52,000 na miyagun ƙwayoyi a bainar jama’a a ƙauyen Karofi da ke Kufena, a kan tsohuwar hanyar Birnin Gwari da ke Zariya.
An gudanar da bikin ƙone kayan ne a wannan Alhamis ɗin, inda Birgediya Janar Buba Marwa (Rtd.), Shugaban NDLEA kuma Babban Jami’in Gudanarwa, ya jaddada cewa hukumar ta duƙufa domin kawar da barazanar miyagun ƙwayoyi daga cikin al’umma.
Ina girmama sojojin Nijeriya — Wike Bebejin Katsina, Alhaji Nuhu Yashe ya rasuYa bayyana cewa, “Miyagun ƙwayoyi suna lalata tarbiyyar matasa a hankali, ba tare da an farga ba. Kowace tan ɗaya da aka ƙone, an ceto rayukan mutane da dama daga halaka.”
Shugaban hukumar, wanda Mataimakin Daraktan Harkokin Miyagun ƙwayoyi, Suleiman Ningi, ya wakilta, ya yi gargadi ga masu safarar miyagun ƙwayoyi da su daina kasuwancin kayan haram, su koma safarar kayan halal, ko kuma su fuskanci hukunci mai tsanani.
Janar Marwa ya ce NDLEA na ci gaba da fatattakar manyan dillalan miyagun ƙwayoyi da ƙungiyoyin su, tare da ƙarfafa wayar da kai a kan illolin kayan laifi.
Ya yaba wa rundunar NDLEA ta Jihar Kaduna bisa ƙoƙarinta, tare da gode wa Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, saboda goyon bayan da yake bayarwa, ciki har da ba da motocin aiki da fili domin gina bariki ga hukumar.
Shugaban NDLEA ya roƙi iyaye, shugabannin al’umma da na addini, da su ƙara ƙaimi wajen wayar da kan mutane kan illar ta’ammali da miyagun ƙwayoyi, yana mai cewa, “Yaƙin da ake yi da miyagun ƙwayoyi yaƙin ceto rayuka da makomar ƙasa ne.”
Kwamandan NDLEA na Jihar Kaduna, Mohammed Tukur, ya bayyana cewa bikin ƙone miyagun ƙwayoyi na nuna jajircewar hukumar wajen kare al’umma daga illolin sha da safarar su.
Ya ce wannan mataki shi ne “ƙarshe a jerin matakan aiwatar da doka”, domin tabbatar da cewa waɗannan ƙwayoyi masu haɗari sun ɓace gaba ɗaya daga hannun mutane, don hana su cutar da matasa ko ƙarfafa ayyukan laifi.
Kwamandan ya bayyana cewa miyagun ƙwayoyin da aka ƙone sun haɗa da Tramadol, Wiwi (Cannabis), da Hodar Iblis da an kiyasta darajar su za ta kai Naira biliyan biyar.
Ya bayyana cewa wannan gagarumar nasara ta samu ne sakamakon ƙoƙarin jami’an NDLEA tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro irin su sojoji, hukumar kwastam, DSS, da ‘yan sanda.
Ya ce, “Wannan aiki shaida ce ta gaskiya, riƙon amana, da ƙwarewar NDLEA. A yau, muna sake tabbatar da sakonmu cewa Jihar Kaduna ba mafakar masu safarar ko masu amfani da miyagun ƙwayoyi ba ce.”
Tukur ya jaddada biyayyarsu wajen dawo da zaman lafiya da kare makomar matasan jihar.
A nasa jawabin, Gwamna Uba Sani ya yaba wa NDLEA bisa ƙoƙarinta wajen ganin cewa an tsarkake Jihar Kaduna daga miyagun ƙwayoyi.
Gwamnan ya ce yawan ƙwayoyin da aka ƙone na nuna tsananin ƙoƙarin da ake yi wajen tabbatar da doka a jihar, tare da jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa dukkan hukumomin tsaro wajen yaƙi da laifuka da duk wata barazanar tsaron al’umma a jihar.