Xi Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Shugaban Namibia Na Farko
Published: 10th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya mika sakon ta’aziyya ga takwaransa na Namibia, Nangolo Mbumba, bisa rasuwar shugaban kasar na farko, Sam Nujoma.
A madadin gwamnati da al’ummar Sinawa, shugaba Xi Jinping ya bayyana jimami tare da yin ta’aziyya ga iyalan Nujoma da ma gwamnati da al’ummar kasar Nambia.
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
Shugaban kungiyar hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’imKasim ya bayyana cewa, kungiyarsa tare da Sojojin kasar da kuma mutanen kasar ne zasu tabbatar da ci gaban kasar Lebanon a wannan halin da ake ciki.
Tashar talabijin ta Al-Mayadeen ta nakalto sheikh Na’im kasim yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar a jiya Litinin, jawabinda kafafen yada labarai da damaa suka watsa kai tsaye.
Sheikh Qasim kasar Lebanon zata ci gaba da zama mai karfi idan gwamnatin kasar ta dakatar da hare-haren da HKI take ci gaba da kawowa a kan kasar, da kwato dukkan yankunan kasar da aka mamaye, har’ila yau da kuma ci gaba da hadin kai tsakanin masu gwagwarmaya, sojoji da kuma mutanen kasar.
Shugaban kungiyar ya jadda bukatar sake gina wuraren da HKI ta rusa a yankunan daban daban a kasar, ya ce gwamnatin kasar ta yi alkawalin zata sake gina wuraren da HKI ta rusa a yakin da hizbullah a baya-bayan nan.
Kuma ya ce rashin yin haka nuna bambanci ne a tsakanin mutanen kasar. Ya ce dangane da wadanda aka rusa gidajensu kungiyar ta bada kudaden haya ga 50,755 , sannan ta gyura wasu 332 da aka lalata, wanda duk aikin gwamnati ne ta yi hakan. Don haka akwai bukatar gwamnati ta aikata wajibin da ya hau kanta.