Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya zargi bangaren shari’a ta Nijeriya da rashawa, inda ya yi zargin cewa alkalai da lauyoyi da amsar na goro, inda ya ce suna cin amanar aikinsu a yayin da suke shari’a.
Ya shaida hakan ne a lokacin da yake jawabi a wajen bikin makon shari’a, wanda reshen kungiyar lauyoyi ta kasa (NBA) a Bwari da ke Abuja ta shirya, El-Rufai ya ce yanzu ‘yan Nijeriya sun yanke aminci da yarda da suke yi da sashin shari’a sakamakon jinkirin da ake samu na tabbatar da adalci da shigar da son zuciya na kashin kai a maimakon muradin jama’a.
- Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai
- Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
“Haka zalika, bangaren shari’armu, wanda ya kamata ya zama ginshikin wanzar da gaskiya da oda, amma yana fama da matsalolin da suke bukatar a duba. Damuwar da aka samu game da jinkirin shari’a, rashin ingancin tsarin aiki, da kuma wasu lokuta cin amanar shari’a, suna zubar da kwarin gwiwar jama’a,” in ji shi.
Tsohon gwamnan ya koka kan yadda ake yawan samun umarnin kotu na dakatar da ci gaba da shari’a ko kama kan wasu lamuran da suka shafi siyasa, inda ya zargi wasu ma’aikatan shari’a da amfani da tsarin kotuna domin cimma muradi ta siyasa.
Ya kuma sake nuna damuwa kan yadda ake samun rashin daidaito a bangaren shari’a da adalci a fadin kasar nan, yana mai nuna cewa bangaren shari’a ya zama dandalin kare muradun gwamnati mai ci wanda kuma ba hakan ya kamata ba.
El-Rufai ya yi kira ga alkalai da lauyoyi da su ji tsoron Allah su koma kan asalin aikin da ke gabansu tare da himmatuwa wajen wanzar da adalci da gaskiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp