• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

by Sulaiman
4 weeks ago
in Labarai
0
Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce shirye-shiryen Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata suna ƙarfafa tushen farfaɗowar tattalin arzikin Nijeriya ta hanyar sauye-sauye masu ƙarfi, da zuba jari mai ma’ana da kuma manufofi da suka rungumi kowa da kowa.

 

A yayin da yake gabatar da jawabi a taron Makon Hulɗa Da Jama’a na Nijeriya (NPRW) na shekarar 2025 a Uyo, babban birnin Jihar Akwa Ibom, ministan ya ce hanyoyin da gwamnatin Tinubu ta ɗauka sun sake daidaita tafiyar Nijeriya zuwa babban gyaran tattalin arziki da ke nuna alamun nasara a fannoni da dama.

  • Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo
  • Na Kwana A Marte Ne Don Ƙarfafa Gwiwar Jama’a Bayan Harin Boko Haram – Zulum

Ya ce: “Ku ba ni dama in bayyana tare da cikakken yaƙini cewa Ajandar Sabunta Fata tana shimfiɗa hanya mai ƙarfi zuwa farfaɗowar tattalin arzikin Nijeriya.”

 

Labarai Masu Nasaba

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

Ya ƙara da cewa, “Kuma wajibi ne a gare mu, a matsayin mu na ƙwararrun ma’aikatan hulɗa da jama’a, mu daidaita da wannan lokaci ta hanyar amfani da dabarun sadarwa masu ɗauke da ƙwarewa, ƙima, da haɗin kai, domin ƙarfafa gwiwar al’ummar mu, a gida da waje, su shiga cikin farfaɗo da tattalin arzikin wannan babbar ƙasa.”

 

Idris ya bayyana cewa aikin sake fasalin tattalin arziki ya faro ne tun daga ranar farko da Shugaban Ƙasa Tinubu ya hau mulki, lokacin da aka cire tallafin man fetur da kuma daidaita farashin musayar kuɗi — matakan da ya bayyana a matsayin “tushen farfaɗowar tattalin arzikin ƙasar nan.”

 

Ya haƙƙaƙe da cewa waɗannan matakai sun haifar da wahalhalu da farko, amma yanzu an fara ganin alfanun su, ciki kuwa har da daidaituwar musayar kuɗi, da ƙaruwar kuɗaɗen shiga ga jihohi, da farfaɗowar masana’antun tace mai, da kuma ƙarfafa matsayin kuɗin gwamnati.

 

Yayin da gwamnatin Tinubu take da da cika shekara biyu, ministan ya bayyana cewa ‘yan Nijeriya suna ganin gagarumin zuba jari da ake yi a harkar ababen more rayuwa, noma, tsaro, da bunƙasa rayuwar ɗan’adam.

 

A cewar sa, an ware naira tiriliyan 2.5 don ayyukan gina manyan hanyoyi a 2025 — adadin da ya fi na kowanne lokaci a tarihin Nijeriya.

 

Ya kuma bayyana ƙirƙirar sababbin ma’aikatu na bunƙasa yankuna da na kiwon dabbobi, domin ƙara bunƙasa arzikin ƙasa da noma da aka yi, da kuma ƙaddamar da shirin lamuni na NELFUND wanda ya taimaka wa ɗaliban Nijeriya sama da 300,000 da kuɗin karatu da gudanar da rayuwar su.

 

Daga cikin sauran muhimman ayyuka da ministan ya lissafa akwai shirin Shugaban Ƙasa na amfani da iskar gas ta CNG a motoci wanda ya jawo zuba jari kai-tsaye na fiye da dalar Amurka miliyan 450; da kafa CreditCorp domin bai wa ‘yan Nijeriya damar samun rance don gina gidajen su da kula da lafiyar su; da kuma ware naira biliyan 200 don tallafa wa ƙananan ‘yan kasuwa, ƙananan sana’o’i (SMEs) da manyan masana’antu.

 

Ya ƙara da cewa: “Yanzu haka Nijeriya ta zama wani gagarumin wurin gine-gine, inda aka kasafta sama da naira tiriliyan 2.5 don gudanar da ayyukan hanyoyi a wannan shekara kaɗai — wanda hakan bai taɓa faruwa ba a tarihin ƙasar nan.

 

“Gwamnati tana haɗa birane ta hanyar manyan ayyuka irin su hanyar Legas zuwa Kalaba da wata hanyar daga Badagry zuwa Sakkwato, da sauran sassa na ƙasa.

 

“Akwai sauran ayyuka da dama da ke gudana yanzu haka. Daga farfaɗowar matatun mai na Fatakwal da Warri, zuwa amincewa da a kashe naira biliyan 80 don sake gina dam ɗin Alau da ke Jihar Borno, zuwa ci gaban aikin gina layin dogo na zamani daga Kano zuwa Kaduna — babu wani yanki na ƙasar da aka bari a baya a cikin wannan babban zuba jari a ababen more rayuwa ƙarƙashin Shugaban Ƙasa Tinubu, wanda yanzu ake kira ‘The Road Master.’”

 

Ministan ya kuma nuna wasu alamomin da ke nuna bunƙasar tattalin arziki inda ya ce, “Ma’aunin Canjin Farashin Kayayyaki (CPI) na watan Afrilu 2025, wanda Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa ta fitar kwanan nan, ya nuna cewa hauhawar farashi ya tsaya a kashi 23.71, wanda an samu raguwar kashi 0.52 daga kashi 24.23 da aka samu a watan Maris. Wannan bai faru ba sai saboda tsare-tsaren Shugaban Ƙasa, waɗanda yanzu haka sun fara bayyana kuma suna haifar da ɗa mai ido.”

 

Idris ya buƙaci ƙwararrun masanan hulɗar jama’a da su taka rawar gani wajen gina da kuma nuna sabuwar martabar tattalin arzikin Nijeriya ga duniya.

 

“Nijeriya tana bunƙasa!” inji shi. “Nijeriya ta jawo fiye da dalar Amurka biliyan 50 na sababbin hannun jari kai-tsaye daga ƙasashen waje, kuɗin da ‘yan Nijeriya suke turowa daga ƙetare sun kai dala biliyan 21.9, kuma masana’antar finafinai (Nollywood) ta bayar da gudunmawar fiye da naira biliyan 730 ga haɓakar tattalin arziki (GDP).

 

“Waɗannan ba ƙididdiga ba ne kawai — su ne labarai da suke buƙatar a bada su ta hanya mai kyau, bisa ƙwarewa, kuma cikin ƙaunar ƙasa.”

 

Idris ya jaddada cewa ma’aikatar sa za ta ci gaba da inganta saƙonnin ƙasa ta hanyar sabon tsarin sadarwa na ƙasa mai suna National Strategic Communication Framework (NSCF).

 

Ya kuma taya Shugaban Hukumar NIPR, Dakta Ike Neliaku, murna bisa zaɓen sa a matsayin Wakilin Lardi na Musamman (Regional Delegate-at-Large) na ƙungiyar Global Alliance for PR and Communication Management.

 

Ya ce: “Ina taya ka murna, ya Shugaban mu, bisa wannan gagarumar nasara. A ƙarƙashin jagorancin ka, aikin hulɗar jama’a ya samu ƙarin daraja sosai a gida da wajen Nijeriya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Next Post

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

Related

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
Manyan Labarai

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

2 hours ago
Kawayen amarya
Manyan Labarai

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

11 hours ago
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
Labarai

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

11 hours ago
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri
Labarai

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

14 hours ago
EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
Manyan Labarai

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

15 hours ago
Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
Labarai

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

17 hours ago
Next Post
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

LABARAI MASU NASABA

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

June 19, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

June 18, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

June 18, 2025
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

June 18, 2025
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.